< Zacharie 1 >

1 Le huitième mois, en la deuxième année de Darius, la parole de Yahweh fut adressée à Zacharie, fils de Barachie, petit-fils d’Addo, le prophète, en ces termes:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 Yahweh a été dans un grand courroux contre vos pères.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Et tu leur diras: Ainsi parle Yahweh des armées: Revenez à moi, — oracle de Yahweh des armées, et je reviendrai à vous, — dit Yahweh des armées.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Ne soyez pas comme vos pères, auxquels ont prêché les premiers prophètes en disant: « Ainsi parle Yahweh des armées: Revenez donc de vos mauvaises voies, et de vos mauvaises actions! » et qui n’ont pas écouté et ne m’ont pas prêté attention, — oracle de Yahweh.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Vos pères, où sont-ils? Et les prophètes, pouvaient-ils vivre éternellement?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Mais mes paroles et mes décrets, dont j’avais chargé mes serviteurs les prophètes, n’ont-ils pas atteint vos pères, si bien qu’ils se sont convertis et ont dit: « Comme Yahweh des armées avait résolu d’agir à notre égard, selon nos voies et selon nos actions, ainsi il a agi envers nous. »
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 Le vingt-quatrième jour du onzième mois, qui est le mois de Sabath, en la deuxième année de Darius, la parole de Dieu fut adressée à Zacharie, fils de Barachie, petit-fils d’Addo, le prophète, en ces termes:
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 J’ai eu une vision pendant la nuit: Voici qu’un homme était monté sur un cheval roux, et il se tenait entre des myrtes dans un lieu ombragé, et il y avait derrière lui des chevaux roux, alezans et blancs.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 Je dis: « Que sont ceux-ci, mon seigneur? » Et l’ange qui parlait avec moi me dit: « Je te ferai voir ce que sont ceux-ci. »
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 Et l’homme qui se tenait entre les myrtes prit la parole et dit: « Ce sont ceux que Yahweh a envoyés pour parcourir la terre. »
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 Et ils répondirent à l’ange de Yahweh qui se tenait entre les myrtes, et ils dirent: « Nous avons parcouru la terre, et voici que toute la terre est habitée et tranquille. »
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 L’ange de Yahweh prit la parole et dit: « Yahweh des armées, jusques à quand n’auras-tu pas pitié de Jérusalem et des villes de Juda contre lesquelles tu es irrité voilà soixante-dix ans? »
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 Et Yahweh adressa à l’ange qui parlait avec moi de bonnes paroles, des paroles de consolation.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 Et l’ange qui parlait avec moi me dit: « Proclame ceci: Ainsi parle Yahweh des armées: J’ai été animé d’une grande jalousie pour Jérusalem et pour Sion;
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 et je suis animé d’un grand courroux contre les nations qui vivent dans l’opulence! Car moi, j’étais un peu irrité; et elles ont, elles, travaillé à la ruine.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 C’est pourquoi ainsi parle Yahweh: Je reviens à Jérusalem avec compassion; ma maison y sera rebâtie, — oracle de Yahweh des armées, et le cordeau sera étendu sur Jérusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Proclame encore ceci: Ainsi parle Yahweh des armées: Mes villes regorgeront encore de biens, et Yahweh consolera encore Sion, et choisira encore Jérusalem. »
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Je levai les yeux et je vis: Et voici quatre cornes.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 Et je dis à l’ange qui parlait avec moi: « Que sont celles-ci? » Il me dit: « Ce sont les cornes qui ont dispersé Juda, Israël et Jérusalem. »
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 Et Yahweh me fit voir quatre forgerons.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 Et je dis: « Que viennent faire ceux-ci? » Il répondit en ces termes: « Ce sont là les cornes qui ont dispersé Juda, au point que personne ne levait la tête, et ceux-ci sont venus pour les frapper de terreur, pour abattre les cornes des nations qui ont levé la corne contre le pays de Juda pour le disperser.
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”

< Zacharie 1 >