< Ruth 4 >

1 Booz monta à la porte de la ville et s’y assit. Or voici que celui qui avait droit de rachat et dont Booz avait parlé, vint à passer. Il lui dit: « Arrête-toi, assieds-toi ici, toi un tel. » Cet homme s’arrêta et s’assit.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Alors Booz prit dix hommes parmi les anciens de la ville, et il dit: « Asseyez-vous ici. » Et ils s’assirent.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Il dit à celui qui avait le droit de rachat: « La portion de champ qui appartenait à notre frère Élimélech, a été vendue par Noémi, qui est revenue des champs de Moab.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Et j’ai dit: je veux t’en informer et te dire: Achète-la en présence de ceux qui siègent ici, et en présence des anciens de mon peuple. Si tu veux racheter, rachète; si tu ne veux pas, déclare-le-moi, afin que je le sache; car il n’y a personne avant toi qui ait le droit de rachat; moi, je viens après toi. » Il répondit: « Je rachèterai. »
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Et Booz dit: « Le jour où tu acquerras le champ de la main de Noémi, tu l’acquerras en même temps de Ruth la Moabite, femme du défunt, pour faire revivre le nom du défunt dans son héritage. »
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Celui qui avait le droit de rachat répondit: « Je ne puis pas le racheter pour mon compte, de peur de détruire mon propre héritage. Fais usage de mon droit de rachat, car je ne puis racheter. »
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 C’était autrefois la coutume en Israël, en cas de rachat et d’échange, pour valider toute affaire, que l’homme ôtât son soulier et le donnât à l’autre cela servait de témoignage en Israël.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Celui qui avait le droit de rachat dit à Booz « Acquiers pour ton compte. » Et il ôta son soulier.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Et Booz dit aux anciens et à tout le peuple: « Vous êtes témoins aujourd’hui que j’ai acquis de la main de Noémi tout ce qui appartenait à Élimélech, et tout ce qui appartenait à Cheljon et à Mahalon,
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 et que j’ai acquis en même temps pour femme Ruth la Moabite, femme de Mahalon, pour faire revivre le nom du défunt dans son héritage, afin que le nom du défunt ne soit pas retranche d’entre ses frères et de la porte de son lieu. Vous en êtes témoins en ce jour! »
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Tout le peuple qui était à la porte et les anciens dirent: « Nous en sommes témoins. Que Yahweh rende la femme qui entre dans ta maison semblable à Rachel et à Lia, qui toutes les deux ont bâti la maison d’Israël! Sois fort dans Ephrata, et fais-toi un nom dans Bethléem!
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 Puisse ta maison être semblable à la maison de Pharès, — que Thamar enfanta à Juda, — par la postérité que Yahweh te donnera de cette jeune femme! »
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Booz prit Ruth, et elle fut sa femme, et il alla vers elle. Yahweh donna à Ruth de concevoir, et elle enfanta un fils.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Les femmes dirent à Noémi: « Béni soit Yahweh, qui ne t’a pas laissé manquer aujourd’hui d’un rédempteur! Que son nom devienne célèbre en Israël!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 Il restaurera ton âme et sera le soutien de ta vieillesse! Car ta belle-fille, qui t’aime, l’a enfanté, elle qui vaut mieux pour toi que sept fils. »
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 Noémi prit l’enfant, le mit sur son sein, et elle lui servit de nourrice.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 Les voisines lui donnèrent un nom, en disant: « Un fils est né à Noémi! » Et elles l’appelèrent Obed. Ce fut le père d’Isaï, père de David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Voici la postérité de Pharès: Pharès engendra Esron;
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 Esron engendra Aram; Aram engendra Aminadab;
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 Aminadab engendra Nahasson; Nahasson engendra Salmon;
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 Salmon engendra Booz; Booz engendra Obed;
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 Obed engendra Isaï: Isaï engendra David. »
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >