< Psaumes 75 >

1 Au maître de chant. « Ne détruis pas! » Psaume d’Asaph. Cantique. Nous te louons, ô Dieu, nous te louons; ton nom est proche: on raconte tes merveilles.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 « Quand le temps sera venu, je jugerai avec justice.
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 La terre est ébranlée avec tous ceux qui l’habitent; moi, j’affermis ses colonnes. » — Séla.
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 Je dis aux orgueilleux: Ne vous enorgueillissez pas! et aux méchants: Ne levez pas la tête!
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 Ne levez pas si haut la tête, ne parlez pas avec tant d’arrogance!
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 Car ce n’est ni de l’orient, ni de l’occident; ni du désert des montagnes!...
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 Non; c’est Dieu qui exerce le jugement: il abaisse l’un et il élève l’autre.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 Car il y a dans la main de Yahweh une coupe, où bouillonne un vin plein d’aromates. Et il en verse: oui, ils en suceront la lie, ils boiront, tous les méchants de la terre.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 Et moi, je publierai à jamais, je chanterai les louanges du Dieu de Jacob.
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 Et j’abattrai toutes les cornes des méchants; et les cornes du juste seront élevées.
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”

< Psaumes 75 >