< Psaumes 7 >

1 Dithyrambe de David, qu’il chanta à Yahweh à l’occasion des paroles de Chus, le Benjamite. Yahweh, mon Dieu, en toi je me confie; sauve-moi de tous mes persécuteurs et délivre-moi,
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 de peur qu’il ne me déchire, comme un lion, qu’il ne dévore sa proie, sans que nul ne la lui arrache.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Yahweh, mon Dieu, si j’ai fait cela, s’il y a de l’iniquité dans mes mains;
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 si j’ai rendu le mal à qui est en paix avec moi, si j’ai dépouillé celui qui m’opprime sans raison,
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 que l’ennemi me poursuive et m’atteigne, qu’il foule à terre ma vie, qu’il couche ma gloire dans la poussière.
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Lève-toi, Yahweh, dans ta colère, porte-toi contre les fureurs de mes adversaires; réveille-toi pour me secourir, toi qui ordonnes un jugement.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 Que l’assemblée des peuples t’environne! Puis, t’élevant au-dessus d’elle, remonte dans les hauteurs.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 Yahweh juge les peuples: rends-moi justice, Yahweh, selon mon droit et mon innocence.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 Mets un terme à la malice des méchants, et affermis le juste, toi qui sondes les cœurs et les reins, ô Dieu juste!
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Mon bouclier est en Dieu, qui sauve les hommes au cœur droit.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 Dieu est un juste juge; tous les jours, le Tout-Puissant fait entendre ses menaces.
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Certes, de nouveau il aiguise son glaive, il bande son arc et il vise;
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 il dirige sur lui des traits meurtriers, il rend ses flèches brûlantes.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Voici le méchant en travail de l’iniquité: il a conçu le malheur, et il enfante le mensonge.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 il ouvre une fosse, il la creuse, et il tombe dans l’abîme qu’il préparait.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 Son iniquité retombe sur sa tête, et sa violence redescend sur son front.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 Je louerai Yahweh pour sa justice, je chanterai le nom de Yahweh, le Très-Haut.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psaumes 7 >