< Psaumes 50 >

1 Psaume d’Asaph. Dieu, Elohim, Yahweh parle et convoque la terre, du lever du soleil à son couchant.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 De Sion, beauté parfaite, Dieu resplendit.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Il vient, notre Dieu, et il ne se taira point; devant lui est un feu dévorant, autour de lui se déchaîne la tempête.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Il appelle les cieux en haut, et la terre, pour juger son peuple:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 « Rassemblez-moi mes fidèles, qui ont fait alliance avec moi sur le sacrifice. »
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Et les cieux proclament sa justice, car c’est Dieu qui va juger. — Séla.
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 « Ecoute, mon peuple, et je parlerai; Israël, et je te reprendrai: je suis Elohim, ton Dieu.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Ce n’est pas pour tes sacrifices que je te blâme; tes holocaustes sont constamment devant moi.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 je ne prendrai pas un taureau dans ta maison, ni des boucs dans tes bergeries.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Car à moi sont tous les animaux des forêts, toutes les bêtes des montagnes par milliers;
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 je connais tous les oiseaux des montagnes, et ce qui se meut dans les champs est sous ma main.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Si j’avais faim, je ne te le dirai pas, car le monde est à moi, et tout ce qu’il renferme.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Est-ce que je mange la chair des taureaux? Est-ce que je bois le sang des boucs?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Offre en sacrifice à Dieu l’action de grâces, et acquitte tes vœux envers le Très-Haut.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Et invoque-moi au jour de la détresse: je te délivrerai, et tu me glorifieras. »
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Mais au méchant Dieu dit: « Quoi donc! tu énumères mes préceptes, et tu as mon alliance à la bouche,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 toi qui détestes la discipline, et qui jettes mes paroles derrière toi!
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Si tu vois un voleur, tu te plais avec lui, et tu fais cause commune avec les adultères.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Tu abandonnes ta bouche au mal, et ta langue ourdit la fraude.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Tu t’assieds, et tu parles contre ton frère, tu diffames le fils de ta mère.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Voilà ce que tu as fait, et je me suis tu. Tu t’es imaginé que j’étais pareil à toi; mais je vais te reprendre et tout mettre sous tes yeux. »
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Prenez-y donc garde, vous qui oubliez Dieu, de peur que je ne déchire, sans que personne délivre.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Celui qui offre en sacrifice l’action de grâces m’honore, et à celui qui dispose sa voie je ferai voir le salut de Dieu.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psaumes 50 >