< Psaumes 27 >

1 De David. Yahweh est ma lumière et mon salut: qui craindrais-je? Yahweh est le rempart de ma vie: de qui aurais-je peur?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 Quand des méchants se sont avancés contre moi, pour dévorer ma chair; quand mes adversaires et mes ennemis se sont avancés, ce sont eux qui ont chancelé et qui sont tombés.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Qu’une armée vienne camper contre moi, mon cœur ne craindra point; que contre moi s’engage le combat, alors même j’aurai confiance.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 Je demande à Yahweh une chose, je la désire ardemment: je voudrais habiter dans la maison de Yahweh, tous les jours de ma vie, pour jouir des amabilités de Yahweh, pour contempler son sanctuaire.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 Car il m’abritera dans sa demeure au jour de l’adversité, il me cachera dans le secret de sa tente, il m’établira sur un rocher.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 Alors ma tête s’élèvera au-dessus des ennemis; qui sont autour de moi. J’offrirai dans son tabernacle des sacrifices d’actions de grâces, je chanterai et je dirai des hymnes à Yahweh.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Yahweh, écoute ma voix, je t’invoque; aie pitié de moi et exauce-moi!
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 Mon cœur dit de ta part: « Cherchez ma face «; je cherche ta face, Yahweh.
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Ne me cache pas ta face, ne repousse pas avec colère ton serviteur; tu es mon secours, ne me délaisse pas, et ne m’abandonne pas, Dieu de mon salut!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 Car mon père et ma mère m’ont abandonné, mais Yahweh me recueillera.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Seigneur, enseigne-moi ta voie; dirige-moi dans un sentier uni, à cause de ceux qui m’épient.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Ne me livre pas à la fureur de mes adversaires, car contre moi s’élèvent des témoins de mensonge, et des gens qui ne respirent que violence.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 Ah! si je ne croyais pas voir la bonté de Yahweh, dans la terre des vivants...
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Espère en Yahweh! Aie courage et que ton cœur soit ferme! Espère en Yahweh!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.

< Psaumes 27 >