< Psaumes 18 >

1 Au maître de chant. Psaume du serviteur de Yahweh, de David, qui adressa à Yahweh les paroles de ce cantique, au jour où Yahweh l’eut délivré de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül. Il dit: Je t’aime, Yahweh, ma force!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Yahweh mon rocher, ma forteresse, mon libérateur, mon Dieu, mon roc où je trouve un asile, mon bouclier, la corne de mon salut, ma citadelle!
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 J’invoquai celui qui est digne de louange, Yahweh, et je fus délivré de mes ennemis.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Les liens de la mort m’environnaient, les torrents de Bélial m’épouvantaient,
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 les liens du schéol m’enlaçaient, les filets de la mort étaient tombés devant moi. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 Dans ma détresse, j’invoquai Yahweh, et je criai vers mon Dieu; de son temple il entendit ma voix, et mon cri devant lui parvint à ses oreilles.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 La terre fut ébranlée et trembla, les fondements des montagnes s’agitèrent, et ils furent ébranlés, parce qu’il était courroucé;
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 une fumée montait de ses narines, et un feu dévorant sortait de sa bouche; il en jaillissait des charbons embrasés.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 il abaissa les cieux, et descendit; une sombre nuée était sous ses pieds.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Il monta sur un Chérubin, et il volait; il planait sur les ailes du vent.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Il fit des ténèbres sa retraite, sa tente autour de lui c’étaient des eaux obscures et de sombres nuages.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 De l’éclat qui le précédait s’élancèrent ses nuées, portant la grêle et les charbons ardents.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Yahweh tonna dans les cieux, le Très-Haut fit retentir sa voix: grêle et charbons ardents!
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 Il lança ses flèches et les dispersa; il multiplia ses foudres et il les confondit.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Alors le lit des eaux apparut, les fondements de la terre furent mis à nu, à ta menace, Yahweh, au souffle du vent de tes narines.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 Il étendit sa main d’en haut et me saisit, il me retira des grandes eaux.
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 Il me délivra de mon ennemi puissant, de ceux qui me haïssaient, alors qu’ils étaient plus forts que moi.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 Ils m’avaient surpris au jour de mon malheur; mais Yahweh fut mon appui.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 Il m’a mis au large, il m’a sauvé, parce qu’il s’est complu en moi.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 Yahweh m’a récompensé selon ma justice, il m’a rendu selon la pureté de mes mains.
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 Car j’ai gardé les voies de Yahweh, et je n’ai pas péché, pour m’éloigner de mon Dieu.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 Tous ses jugements étaient devant moi, et je n’ai pas rejeté loin de moi ses lois.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 J’étais sans reproche envers lui, et je me tenais en garde contre mon iniquité.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Yahweh m’a rendu selon ma justice, selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Avec celui qui est bon tu te montres bon, avec l’homme droit tu te montres droit;
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 avec celui qui est pur tu te montres pur, et avec le fourbe tu agis perfidement.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 Car tu sauves le peuple humilié, et tu abaisses les regards hautains.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 Oui, tu fais briller mon flambeau; Yahweh, mon Dieu, éclaire mes ténèbres.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 Avec toi je me précipite sur les bataillons armés; avec mon Dieu je franchis les murailles.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Dieu!... Ses voies sont parfaites; la parole de Yahweh est éprouvée, il est un bouclier pour tous ceux qui se confient en lui.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Car qui est Dieu, si ce n’est Yahweh, et qui est un rocher, si ce n’est notre Dieu?
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 Le Dieu qui me ceint de force, qui rend ma voie parfaite;
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 qui rend mes pieds semblables à ceux des biches, et me fait tenir debout sur mes hauteurs;
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 qui forme mes mains au combat, et mes bras tendent l’arc d’airain.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Tu m’as donné le bouclier de ton salut, et ta droite me soutient, et ta douceur me fait grandir.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Tu élargis mon pas au-dessous de moi, et mes pieds ne chancellent point.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 Je poursuis mes ennemis et je les atteins; je ne reviens pas sans les avoir anéantis.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 Je les brise, et ils ne se relèvent pas; Ils tombent sous mes pieds.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Tu me ceins de force pour le combat, tu fais plier sous moi mes adversaires.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 Mes ennemis!... tu leur fais tourner le dos devant moi, et j’extermine ceux qui me haïssent.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 Ils crient, et personne pour les sauver! Ils crient vers Yahweh, et il ne leur répond pas!
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Je les broie comme la poussière livrée au vent, je les balaie comme la boue des rues.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Tu me délivres des révoltes du peuple, tu me mets à la tête des nations; Des peuples que je ne connaissais pas me sont asservis.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 Dès qu’ils ont entendu, ils m’obéissent; les fils de l’étranger me flattent.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Les fils de l’étranger sont défaillants, ils sortent tremblants de leurs forteresses.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 Vive Yahweh et béni soit mon rocher! Que le Dieu de mon salut soit exalté;
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 Dieu qui m’accorde des vengeances, qui me soumet les peuples,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 qui me délivre de mes ennemis! Oui, tu m’élèves au-dessus de mes adversaires, tu me sauves de l’homme de violence.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 C’est pourquoi je te louerai parmi les nations, ô Yahweh; je chanterai à la gloire de ton nom:
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 Il accorde de glorieuses délivrances à son roi, il fait miséricorde à son oint, à David et à sa postérité pour toujours.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< Psaumes 18 >