< Psaumes 16 >

1 Hymne de David. Garde-moi ô Dieu, car près de toi je me réfugie.
Miktam ne na Dawuda. Ka kiyaye ni, ya Allah, gama a cikinka nake samun mafaka.
2 Je dis à Yahweh: « Tu es mon Seigneur, toi seul es mon bien. »
Na ce wa Ubangiji, “Kai ne shugabana; in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau.”
3 Les saints qui sont dans le pays, ces illustres, sont l’objet de toute mon affection.
Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa, su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.
4 On multiplie les idoles, on court après les dieux étrangers; je ne répandrai pas leurs libations de sang, je ne mettrai pas leurs noms sur mes lèvres.
Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli. Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba ko in ambaci sunayensu da bakina.
5 Yahweh est la part de mon héritage et de ma coupe, c’est toi qui m’assures mon lot.
Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na; ka kiyaye rabona,
6 Le cordeau a mesuré pour moi une portion délicieuse; oui, un splendide héritage m’est échu.
Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi; tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.
7 Je bénis Yahweh qui m’a conseillé; la nuit même, mes reins m’avertissent.
Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara; ko da dare ma zuciyata kan koya mini.
8 Je mets Yahweh constamment sous mes yeux, car il est à ma droite: je ne chancellerai point.
Kullum nakan sa Ubangiji a gabana. Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.
9 Aussi mon cœur est dans la joie, mon âme dans l’allégresse, mon corps lui-même repose en sécurité.
Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki; jikina kuma zai zauna lafiya,
10 Car tu ne livreras pas mon âme au schéol, tu ne permettras pas que celui qui t’aime voie la corruption. (Sheol h7585)
domin ba za ka yashe ni a kabari ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Sheol h7585)
11 Tu me feras connaître le sentier de la vie; il y a plénitude de joie devant ta face, des délices éternelles dans ta droite.
Ka sanar da ni hanyar rai; za ka cika ni da farin ciki a gabanka, da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.

< Psaumes 16 >