< Psaumes 122 >
1 Cantique des montées. De David. J’ai été dans la joie quand on m’a dit: « Allons à la maison de Yahweh! »
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Enfin! Nos pieds s’arrêtent à tes portes, Jérusalem!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jérusalem, tu es bâtie comme une ville où tout se tient ensemble.
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Là montent les tribus, les tribus de Yahweh, selon la loi d’Israël, pour louer le nom de Yahweh.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 Là sont établis des sièges pour le jugement, les sièges de la maison de David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Faites des vœux pour Jérusalem: Qu’ils soient heureux ceux qui t’aiment!
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Que la paix règne dans tes murs, la prospérité dans tes palais!
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 A cause de mes frères et de mes amis, je demande pour toi la paix;
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 à cause de la maison de Yahweh, notre Dieu, je désire pour toi le bonheur.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.