< Nombres 9 >

1 Yahweh parla à Moïse, dans le désert de Sinaï, le premier mois de la deuxième année après leur sortie du pays d’Égypte. Il dit:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
2 « Que les enfants d’Israël fassent la Pâque au temps fixé.
“Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
3 Vous la ferez au temps fixé, le quatorzième jour de ce mois, entre les deux soirs: c’est le temps fixé; vous la ferez selon toutes les lois et toutes les ordonnances qui la concernent. »
A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
4 Moïse parla donc aux enfants d’Israël, afin qu’ils fissent la Pâque.
Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
5 Et ils firent la Pâque le quatorzième jour du premier mois, entre les deux soirs, dans le désert de Sinaï. Selon tout ce que Yahweh avait ordonné à Moïse, ainsi firent les enfants d’Israël.
suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Il y eut des hommes qui se trouvaient impurs à cause d’un cadavre et qui ne purent faire la Pâque ce jour-là. S’étant présentés le jour même devant Moïse et Aaron,
Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
7 ils dirent à Moïse: « Nous sommes impurs à cause d’un cadavre; pourquoi serions-nous privés de présenter l’offrande de Yahweh, au temps fixé, au milieu des enfants d’Israël? »
suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
8 Moïse leur répondit: « Attendez que j’apprenne ce que Yahweh vous ordonnera. »
Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
9 Yahweh parla à Moïse, en disant:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
10 « Parle aux enfants d’Israël et dis-leur: Si quelqu’un, parmi vous ou parmi vos descendants, se trouve impur à cause d’un cadavre ou est en voyage au loin, il fera la Pâque en l’honneur de Yahweh.
“Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
11 C’est au second mois qu’ils la feront, le quatorzième jour, entre les deux soirs; ils la mangeront avec des pains sans levain et des herbes amères.
Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
12 Ils n’en laisseront rien jusqu’au matin, et ils n’en briseront pas les os. Ils la célébreront selon toutes les prescriptions relatives à la Pâque.
Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
13 Si quelqu’un, étant pur et n’étant pas en voyage, omet de faire la Pâque, il sera retranché de son peuple; parce qu’il n’a pas présenté l’offrande de Yahweh au temps fixé, il portera son péché.
Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
14 Si un étranger séjournant chez vous fait la Pâque de Yahweh, il observera les lois et ordonnances concernant la Pâque. Il y aura une même loi pour vous, pour l’étranger comme pour l’indigène. »
“‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
15 Le jour où la Demeure fut dressée, la nuée couvrit la Demeure: qui est la tente du témoignage; depuis le soir jusqu’au matin, il y eut sur la Demeure comme l’apparence d’un feu.
A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
16 Il en fut ainsi continuellement: la nuée couvrait la Demeure, et la nuit elle avait l’apparence d’un feu.
Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
17 Quand la nuée s’élevait de dessus la tente, les enfants d’Israël levaient le camp, et, à l’endroit où la nuée s’arrêtait, ils dressaient le camp.
Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
18 Au commandement de Yahweh, les enfants d’Israël levaient le camp, et au commandement de Yahweh ils le dressaient; ils restaient campés tant que la nuée se reposait sur la Demeure.
Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
19 Quand la nuée restait longtemps sur la Demeure, les enfants d’Israël observaient le commandement de Yahweh et ne levaient pas le camp.
Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
20 Il en était de même quand la nuée ne s’arrêtait que peu de jours sur la Demeure: au commandement de Yahweh ils dressaient le camp, et au commandement de Yahweh ils le levaient.
Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
21 Si la nuée se reposait seulement du soir au matin, et s’élevait le matin, ils levaient le camp; ou, si la nuée s’élevait après un jour et une nuit, ils levaient le camp.
Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
22 Si la nuée s’arrêtait sur la Demeure plusieurs jours, un mois ou une année, les enfants d’Israël restaient campés, et ne levaient pas le camp; mais, dès qu’elle s’élevait, ils levaient le camp.
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
23 Au commandement de Yahweh ils dressaient le camp, et au commandement de Yahweh ils levaient le camp; ils observaient le commandement de Yahweh, conformément à l’ordre de Yahweh transmis par Moïse.
Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.

< Nombres 9 >