< Nombres 32 >
1 Les fils de Ruben et les fils de Gad avaient des troupeaux en nombre considérable. Voyant que le pays de Jazer et le pays de Galaad étaient un lieu propre pour les troupeaux,
Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
2 les fils de Gad et les fils de Ruben vinrent auprès de Moïse, d’Eléazar, le prêtre, et des princes de l’assemblée, et ils leur dirent:
Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
3 « Ataroth, Dibon, Jazer, Nemra, Hésebon, Eléalé, Saban, Nébo et Béon,
“Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
4 ce pays que Yahweh a frappé devant l’assemblée d’Israël, est un lieu propre pour les troupeaux, et tes serviteurs ont des troupeaux ».
ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
5 Ils ajoutèrent: « Si nous avons trouvé grâce à tes yeux, que ce pays soit donné en possession à tes serviteurs, et ne nous fais pas passer le Jourdain. »
Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
6 Moïse répondit aux fils de Gad et aux fils de Ruben: « Vos frères iront-ils à la guerre, et vous, resterez-vous ici?
Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
7 Pourquoi découragez-vous les enfants d’Israël de passer dans le pays que Yahweh leur donne?
Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
8 C’est ainsi qu’ont fait vos pères, quand je les envoyai de Cadès-Barné explorer le pays.
Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
9 Ils montèrent jusqu’à la vallée d’Escol et virent le pays, et ils découragèrent les enfants d’Israël d’entrer dans le pays que Yahweh leur donnait.
Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
10 Et la colère de Yahweh s’enflamma ce jour-là, et il jura en disant:
A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
11 Ces hommes qui sont montés de l’Égypte, depuis l’âge de vingt ans et au-dessus, ne verront pas le pays que j’ai promis par serment à Abraham, à Isaac et à Jacob, car ils ne m’ont pas fidèlement suivi,
‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
12 excepté Caleb, fils de Jéphoné, le Cénézéen, et Josué, fils de Nun, qui ont suivi fidèlement Yahweh.
ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
13 Et la colère de Yahweh s’enflamma contre Israël, et il les fit errer dans le désert pendant quarante années, jusqu’à ce que fût anéantie toute la génération qui avait fait le mal aux yeux de Yahweh.
Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
14 Et voici que vous prenez la place de vos pères, comme des rejetons de pécheurs, pour accroître encore l’ardeur de la colère de Yahweh contre Israël.
“Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
15 Car si vous refusez de le suivre, il continuera de laisser Israël au désert, et vous causerez la ruine de tout ce peuple. »
In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
16 Ils s’approchèrent de Moïse, et ils dirent: « Nous construirons ici des parcs pour nos troupeaux et des villes pour nos petits enfants;
Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
17 mais nous nous armerons sans tarder pour marcher devant les enfants d’Israël, jusqu’à ce que nous les ayons introduits dans le lieu qu’ils doivent occuper, et nos enfants demeureront dans les villes fortes, à cause des habitants du pays.
Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
18 Nous ne reviendrons pas dans nos maisons, avant que les enfants d’Israël aient pris possession chacun de son héritage;
Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
19 car nous ne posséderons rien avec eux de l’autre côté du Jourdain, ni plus loin, puisque notre héritage nous est venu de ce côté du Jourdain, à l’orient. »
Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
20 Moïse leur dit: « Si vous tenez cette conduite, si vous vous armez pour combattre devant Yahweh;
Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
21 si tous les hommes armés d’entre vous passent le Jourdain devant Yahweh, jusqu’à ce qu’il ait chassé ses ennemis de devant sa face,
in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
22 et que vous ne reveniez qu’après que le pays aura été soumis devant Yahweh, vous serez sans reproche devant Yahweh et devant Israël, et cette contrée-ci sera votre propriété devant Yahweh.
to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
23 Mais si vous n’agissez pas ainsi, voici, vous péchez contre Yahweh; et sachez que votre péché vous atteindra.
“Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
24 Construisez donc des villes pour vos enfants et des parcs pour vos troupeaux, et exécutez la parole qui est sortie de votre bouche. »
Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
25 Les fils de Gad et les fils de Ruben parlèrent à Moïse en disant: « Tes serviteurs feront ce que mon seigneur ordonne.
Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
26 Nos enfants, nos femmes, nos troupeaux et tout notre bétail resteront ici, dans les villes de Galaad;
’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
27 et tes serviteurs, tout homme armé pour combattre, passeront devant Yahweh pour combattre, comme le dit mon seigneur. »
Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
28 Alors Moïse donna des ordres à leur sujet à Eléazar, le prêtre, à Josué, fils de Nun, et aux chefs de famille des tribus des enfants d’Israël;
Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
29 il leur dit: « Si les fils de Gad et les fils de Ruben passent avec vous le Jourdain, tous les hommes armés pour combattre devant Yahweh, et que le pays sois soumis devant vous, vous leur donnerez en possession la conquête de Galaad.
ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
30 Mais s’ils ne passent pas en armes avec vous, ils seront établis au milieu de vous dans le pays de Canaan. »
Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
31 Les fils de Gad et les fils de Ruben répondirent en disant: « Ce que Yahweh a dit à tes serviteurs, nous le ferons.
Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
32 Nous passerons en armes devant Yahweh au pays de Canaan, et la possession de notre héritage nous demeurera de ce côté-ci du Jourdain. »
Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
33 Moïse donna aux fils de Gad et aux fils de Ruben, et à la moitié de la tribu de Manassé, fils de Joseph, le royaume de Séhon, roi des Amorrhéens, et le royaume d’Og, roi de Basan, le pays avec ses villes et leurs territoires, les villes du pays d’alentour.
Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
34 Les fils de Gad bâtirent Dibon, Ataroth, Aroër,
Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
35 Ataroth-Sophan, Jazer, Jegbaa,
Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
36 Bethnemra et Betharan, villes fortes, et ils firent des parcs pour le troupeau.
Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
37 Les fils de Ruben bâtirent Hésebon, Eléalé, Cariathaïm,
Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
38 Nabo et Baalméon, dont les noms furent changés, et Sabama, et ils donnèrent des noms aux villes qu’ils bâtirent.
haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
39 Les fils de Machir, fils de Manassé, allèrent contre Galaad et, s’en étant emparés, ils chassèrent les Amorrhéens qui y étaient.
Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
40 Moïse donna Galaad à Machir, fils de Manassé, qui s’y établit.
Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
41 Jaïr, fils de Manassé, alla et prit leurs bourgs, et il les appela Bourgs de Jaïr.
Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
42 Nobé alla et s’empara de Chanath et des villes de son ressort; il l’appela Nobé, de son nom.
Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.