< Nombres 11 >

1 Le peuple se mit à murmurer du mal aux oreilles de Yahweh. Yahweh l’entendit, et sa colère s’enflamma, et le feu de Yahweh s’alluma contre eux et il dévorait à l’extrémité du camp.
Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
2 Le peuple cria vers Moïse, et Moïse pria Yahweh, et le feu s’éteignit.
Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
3 On donna à ce lieu le nom de Thabéera, parce que le feu de Yahweh s’était allumé contre eux.
Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
4 Le ramas de gens qui se trouvaient au milieu d’Israël s’enflamma de convoitise, et même les enfants d’Israël recommencèrent à pleurer et dirent: « Qui nous donnera de la viande à manger?
Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
5 Il nous souvient des poissons que nous mangions pour rien en Égypte, des concombres, des melons, des poireaux, des oignons et de l’ail.
Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
6 Maintenant notre âme est desséchée; plus rien! Nos yeux ne voient que de la manne. »
Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
7 La manne était semblable à la graine de coriandre, et avait l’aspect du bdellium.
Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
8 Le peuple se répandait pour la ramasser; il la broyait avec des meules ou la pilait dans un mortier; il la cuisait au pot, et en faisait des gâteaux. Elle avait le goût d’un gâteau à l’huile.
Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
9 Quand la rosée descendait pendant la nuit sur le camp, la manne y descendait aussi.
Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
10 Moïse entendit le peuple qui pleurait dans chaque famille, chacun à l’entrée de sa tente. La colère de Yahweh s’enflamma grandement. Moïse fut attristé,
Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
11 et il dit à Yahweh: « Pourquoi avez-vous fait ce mal à votre serviteur, et pourquoi n’ai-je pas trouvé grâce à vos yeux, que vous ayez mis sur moi la charge de tout ce peuple?
Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
12 Est-ce moi qui ai conçu tout ce peuple? est-ce moi qui l’ai enfanté, pour que vous me disiez: Porte-le sur ton sein, comme le nourricier porte un enfant qu’on allaite, jusqu’au pays que vous avez juré à ses pères de lui donner?
Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
13 Où prendrai-je de la viande pour en donner à tout ce peuple? Car ils pleurent autour de moi, en disant: Donne-nous de la viande à manger.
Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
14 Je ne puis pas, à moi seul, porter tout ce peuple; il est trop pesant pour moi.
Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
15 Pour me traiter ainsi, tuez-moi plutôt, je vous prie, si j’ai trouvé grâce à vos yeux, et que je ne voie pas mon malheur! »
In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
16 Yahweh dit à Moïse: « Assemble-moi soixante-dix hommes des anciens d’Israël, que tu connais pour être anciens du peuple et préposés sur lui; amène-les à la tente de réunion et qu’ils se tiennent là avec toi.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
17 Je descendrai et je te parlerai là; je prendrai de l’esprit qui est sur toi et je le mettrai sur eux, afin qu’ils portent avec toi la charge du peuple, et tu ne la porteras plus toi seul.
Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
18 Tu diras au peuple: Sanctifiez-vous pour demain, et vous aurez de la viande à manger, puisque vous avez pleuré aux oreilles de Yahweh, en disant: Qui nous fera manger de la viande? car nous étions bien en Égypte! Et Yahweh vous donnera de la viande, et vous en mangerez;
“Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
19 ce n’est pas un jour que vous en mangerez, ni deux jours, ni cinq jours, ni dix jours, ni vingt jours,
Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
20 mais un mois entier, jusqu’à ce qu’elle vous sorte par les narines et qu’elle vous soit en dégoût, parce que vous avez rejeté Yahweh qui est au milieu de vous, et que vous avez pleuré devant lui, en disant: Pourquoi donc sommes-nous sortis d’Égypte? »
amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
21 Moïse dit: « Le peuple au milieu duquel je suis est de six cent mille hommes de pied, et vous dites: Je leur donnerai de la viande, et ils en mangeront un mois entier!
Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
22 Egorgera-t-on pour eux les brebis et les bœufs, pour qu’ils en aient assez? Ou leur ramassera-t-on tous les poissons de la mer, pour qu’ils en aient assez? »
Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
23 Yahweh répondit à Moïse: « La main de Yahweh est-elle trop courte? Tu verras maintenant si ce que j’ai dit t’arrivera ou non. »
Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
24 Moïse sortit et rapporta au peuple les paroles de Yahweh, et il assembla soixante-dix hommes des anciens du peuple et les plaça autour de la tente.
Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
25 Yahweh descendit dans la nuée et parla à Moïse; il prit de l’esprit qui était sur lui et le mit sur les soixante-dix anciens; et, dès que l’esprit reposa sur eux, ils prophétisèrent; mais ils ne continuèrent pas.
Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
26 Deux hommes, l’un nommé Eldad, et l’autre Médad, étaient restés dans le camp, et l’esprit reposa aussi sur eux; ils étaient parmi les inscrits, mais ils ne s’étaient pas rendus à la tente; et ils prophétisèrent dans le camp.
To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
27 Un jeune garçon courut l’annoncer à Moïse, en disant: « Eldad et Médad prophétisent dans le camp. »
Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
28 Aussitôt Josué, fils de Nun, serviteur de Moïse depuis sa jeunesse, prenant la parole dit: « Moïse, mon seigneur, empêche-les. »
Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
29 Moïse lui répondit: « Es-tu donc jaloux pour moi? Plût à Dieu que tout le peuple de Yahweh fût prophète, et que Yahweh mit son esprit sur eux! »
Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
30 Et Moïse se retira dans le camp, lui et les anciens d’Israël.
Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
31 Un vent souffla de par l’ordre de Yahweh, qui, de la mer, amena des cailles et les abattit sur le camp, sur l’étendue d’environ une journée de chemin d’un côté, d’environ une journée de chemin de l’autre côté, autour du camp; et il y en avait près de deux coudées de haut sur la surface de la terre.
Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
32 Pendant tout ce jour, toute la nuit et toute la journée du lendemain, le peuple se leva et ramassa les cailles; celui qui en avait ramassé le moins en avait dix gomors; et ils les étendirent pour eux, tout autour du camp.
Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
33 Mais la chair était encore entre leurs dents, avant d’être consommée, que la colère de Yahweh s’enflamma contre le peuple, et Yahweh frappa le peuple d’une très grande plaie.
Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
34 On donna à ce lieu le nom de Qibroth-Hattaava, parce qu’on y enterra le peuple qui s’était enflammé de convoitise.
Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
35 De Qibroth-Hattaava le peuple partit pour Haséroth, et il s’arrêta à Haséroth.
Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.

< Nombres 11 >