< Néhémie 1 >

1 Paroles de Néhémie, fils de Helchias. Au mois de Casleu, la vingtième année, comme j’étais à Suse, dans le château,
Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
2 arriva Hanani, l’un de mes frères, avec des hommes de Juda. Je les questionnai au sujet des Juifs délivrés, qui avaient échappé à la captivité, et au sujet de Jérusalem.
Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
3 Ils me répondirent: « Les réchappés, ceux qui ont échappé à la captivité, là-bas dans la province, sont dans une grande misère et dans l’opprobre; les murailles de Jérusalem sont démolies et ses portes consumées par le feu. »
Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
4 Lorsque j’entendis ces choses, je m’assis et je pleurai, et je fus plusieurs jours dans le deuil. Je jeûnais et je priais devant le Dieu du ciel,
Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
5 en disant: « Ah! Yahweh, Dieu du ciel, Dieu grand et redoutable, vous qui gardez l’alliance et la miséricorde à l’égard de ceux qui vous aiment et qui observent vos commandements,
Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
6 que votre oreille soit attentive et que vos yeux soient ouverts, pour que vous entendiez la prière de votre serviteur, celle que je vous adresse maintenant, nuit et jour, pour vos serviteurs, les enfants d’Israël, en confessant les péchés des enfants d’Israël, ceux que nous avons commis contre vous; car moi et la maison de mon père, nous avons péché.
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
7 Nous avons très mal agi envers vous, nous n’avons pas observé les commandements, les lois et les ordonnances que vous avez prescrits à Moïse, votre serviteur.
Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
8 Souvenez-vous de la parole que vous avez ordonné à Moïse, votre serviteur, de prononcer, en disant: Si vous transgressez mes préceptes, je vous disperserai parmi les peuples;
“Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
9 mais si vous revenez à moi, et si vous observez mes commandements et les mettez en pratique, alors même que vos exilés seraient à l’extrémité du ciel, de là je les rassemblerai et je les ramènerai dans le lieu que j’ai choisi pour y faire habiter mon nom.
amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
10 Ils sont vos serviteurs et votre peuple, que vous avez rachetés par votre grande puissance et par votre main forte.
“Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
11 Ah! Seigneur, que votre oreille soit attentive à la prière de votre serviteur et à la prière de vos serviteurs qui se plaisent à craindre votre nom! Daignez aujourd’hui donner le succès à votre serviteur, et faites-lui trouver grâce devant cet homme! » J’étais alors échanson du roi.
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.

< Néhémie 1 >