< Néhémie 13 >

1 En ce temps-là, on lut aux oreilles du peuple dans le livre de Moïse, et l’on y trouva écrit que l’Ammonite et le Moabite ne devaient jamais entrer dans l’assemblée de Dieu,
A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
2 parce qu’ils n’étaient pas venus au-devant des enfants d’Israël avec du pain et de l’eau, et parce qu’ils avaient payé contre eux Balaam pour qu’il les maudit; mais notre Dieu avait changé la malédiction en bénédiction.
domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
3 Lorsqu’on eut entendu cette loi, on sépara d’Israël tous les étrangers.
Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
4 Avant cela, le prêtre Eliasib, qui avait l’intendance des chambres de la maison de notre Dieu et qui était allié de Tobie,
Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
5 avait disposé pour ce dernier une grande chambre où l’on mettait auparavant les offrandes, l’encens, les ustensiles, la dîme du blé, du vin nouveau et de l’huile, la taxe des lévites, des chantres et des portiers, et ce qui était prélevé pour les prêtres.
ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
6 Quand tout cela eut lieu, je n’étais pas à Jérusalem; car, la trente deuxième année d’Artaxerxès, roi de Babylone, j’étais retourné près du roi. Au bout de quelque temps, j’obtins du roi la permission
Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
7 de revenir à Jérusalem, et je m’aperçus du mal qu’avait fait Eliasib, en faveur de Tobie, en arrangeant une chambre pour lui dans les parvis de la maison de Dieu.
sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
8 J’en éprouvai une grande douleur, et je jetai hors de la chambre tous les meubles de la demeure de Tobie.
Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
9 Puis j’ordonnai qu’on purifiât les chambres, et j’y replaçai les ustensiles de la maison de Dieu, les offrandes et l’encens.
Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
10 J’appris aussi que les portions des lévites n’avaient pas été livrées, et que les lévites et les chantres chargés du service s’étaient enfuis chacun dans ses terres.
Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
11 J’adressai des réprimandes aux magistrats, et je dis: « Pourquoi la maison de Dieu est-elle abandonnée? » Et je rassemblai les lévites et les chantres, et je les remis à leur poste.
Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
12 Alors tout Juda apporta dans les magasins la dîme du blé, du vin nouveau et de l’huile.
Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
13 Je confiai l’intendance des magasins à Sélémias, le prêtre, à Sadoc, le scribe, et à Phadaïas, l’un des lévites, et je leur adjoignis Hanan, fils de Zachur, fils de Mathanias, parce qu’ils étaient reconnus fidèles. C’était à eux de faire les distributions à leurs frères.
Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
14 Souvenez-vous de moi, ô mon Dieu, à cause de cela, et n’effacez pas de votre mémoire les actes de piété que j’ai faits pour la maison de Dieu et pour son service!
Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
15 En ce temps là, je vis en Juda des hommes qui foulaient au pressoir pendant le sabbat, qui rentraient des gerbes, chargeaient sur des ânes même du vin, des raisins, des figues et toutes sortes de fardeaux, et qui les amenaient à Jérusalem le jour du sabbat; et je leur donnai un avertissement lorsqu’ils vendaient leurs denrées.
A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
16 De même les Tyriens demeurant à Jérusalem, apportaient du poisson et toutes sortes de marchandises, et les vendaient, le jour du sabbat, aux fils de Juda et dans Jérusalem.
Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
17 J’adressai des réprimandes aux grands de Juda et je leur dis: « Quelle est cette mauvaise action que vous faites, en profanant le jour du sabbat?
Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
18 N’est-ce pas ainsi qu’ont agi vos pères, et n’est-ce pas à cause de cela que notre Dieu a fait venir tous ces malheurs sur nous et sur cette ville? Et vous, vous augmentez encore sa colère contre Israël en profanant le sabbat!... »
Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
19 Ensuite, dès qu’il fit sombre aux entrées de Jérusalem, avant le sabbat, j’ordonnai de fermer les portes, et j’ordonnai qu’on ne les ouvrit qu’après le sabbat. De plus, je plaçai aux portes quelques-uns de mes gens afin qu’aucun fardeau n’entrât le jour du sabbat.
Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
20 Alors les marchands et les vendeurs de toutes sortes de denrées passèrent la nuit une fois ou deux hors de Jérusalem.
Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
21 Je les avertis, et je leur dis: « Pourquoi passez-vous la nuit devant la muraille? Si vous le faites encore, je mettrai la main sur vous. » Depuis ce temps-là, ils ne vinrent plus pendant le sabbat.
Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
22 Et j’ordonnai aux lévites de se purifier et de venir garder les portes pour sanctifier le jour du sabbat. Souvenez-vous encore de moi, ô mon Dieu, à cause de cela, et épargnez-moi selon votre grande miséricorde!
Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
23 En ce même temps, je vis aussi des Juifs qui avaient établi chez eux des femmes azotiennes, ammonites, moabites.
Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
24 La moitié de leurs fils parlaient l’azotien sans pouvoir parler judéen; et de même pour la langue de tel et tel autre peuple.
Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
25 Je leur adressai des réprimandes et je les maudis; j’en frappai plusieurs, je leur arrachai les cheveux et je les adjurai au nom de Dieu, en disant: « Vous ne donnerez pas vos filles à leurs fils et vous ne prendrez pas de leurs filles pour vos fils ou pour vous.
Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
26 N’est-ce pas en cela qu’a péché Salomon, roi d’Israël? Il n’y avait pas de roi semblable à lui parmi la multitude des nations, il était aimé de son Dieu et Dieu l’avait établi roi sur tout Israël; mais les femmes étrangères l’entraînèrent, lui aussi, dans le péché.
Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
27 Fallait-il donc apprendre à votre sujet que vous commettez ce grand crime et que vous péchez contre notre Dieu, en établissant chez vous des femmes étrangères? »
Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
28 Un des fils de Joïada, fils d’Eliasib, le grand prêtre, était gendre de Sanaballat le Horonite; je le chassai loin de moi.
Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
29 Souvenez-vous d’eux, ô mon Dieu, à propos de cette profanation du sacerdoce et des obligations sacrées des prêtres et des lévites!
Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
30 Je les purifiai de tout ce qui était étranger, et je remis en vigueur les règlements concernent les prêtres et les lévites, chacun dans son ministère,
Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
31 et ce qui concernait l’offrande du bois à des époques déterminées, ainsi que les prémices. Souvenez-vous-en en ma faveur, ô mon Dieu, pour mon bien!
Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.

< Néhémie 13 >