< Marc 10 >
1 Étant parti de ce lieu, Jésus vint aux confins de la Judée, au delà du Jourdain; et le peuple s’assembla de nouveau près de lui, et, suivant sa coutume, il recommença à les enseigner.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
2 Les Pharisiens l’ayant abordé lui demandèrent s’il était permis à un mari de répudier sa femme: c’était pour le mettre à l’épreuve.
Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
3 Il leur répondit: « Que vous a ordonné Moïse? »
Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 Ils dirent: « Moïse a permis de dresser un acte de divorce et de répudier. »
Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
5 Jésus leur répondit: « C’est à cause de la dureté de votre cœur qu’il vous a donné cette loi.
Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
6 Mais au commencement de la création, Dieu les fit homme et femme.
Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
7 À cause de cela, l’homme quittera son père et sa mère, et s’attachera à sa femme,
‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
8 et les deux ne feront qu’une seule chair. » Ainsi ils ne sont plus deux, mais ils sont une seule chair.
su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
9 Que l’homme donc ne sépare pas ce que Dieu a uni! »
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
10 Lorsqu’ils furent dans la maison, ses disciples l’interrogèrent encore sur ce sujet,
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11 et il leur dit: « Quiconque répudie sa femme et en épouse une autre, commet un adultère à l’égard de la première.
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12 Et si une femme répudie son mari et en épouse un autre, elle se rend adultère. »
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
13 On lui amena des petits enfants pour qu’il les touchât. Mais les disciples réprimandaient ceux qui les présentaient.
Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
14 Jésus, à cette vue, fut indigné et leur dit: « Laissez les petits enfants venir à moi, et ne les en empêchez pas; car le royaume des cieux est à ceux qui leur ressemblent.
Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
15 Je vous le dis, en vérité, quiconque ne recevra pas comme un petit enfant le royaume de Dieu, n’y entrera point. »
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
16 Puis il les embrassa, et les bénit en leur imposant les mains.
Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
17 Comme il sortait pour se mettre en chemin, quelqu’un accourut, et se jetant à genoux devant lui, lui demanda: « Bon Maître, que dois-je faire pour avoir en héritage la vie éternelle? » (aiōnios )
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios )
18 Jésus lui dit: « Pourquoi m’appelles-tu bon? Il n’y a de bon que Dieu seul.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
19 Tu connais les commandements: Ne commets pas d’adultère, ne tue pas, ne dérobe pas, ne porte pas de faux témoignage, abstiens-toi de toute fraude, honore ton père et ta mère. »
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
20 Il lui répondit: « Maître, j’ai observé toutes ces choses dès ma jeunesse. »
Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
21 Jésus, l’ayant regardé, l’aima et lui dit: « Il te manque une chose; va, vends tout ce que tu as, donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel; puis viens, et suis-moi. »
Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
22 Mais lui, affligé de cette parole, s’en alla tout triste; car il avait de grands biens.
Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
23 Et Jésus, jetant ses regards autour de lui, dit à ses disciples: « Qu’il est difficile à ceux qui ont les biens de ce monde d’entrer dans le royaume de Dieu! »
Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
24 Comme les disciples étaient étonnés de ses paroles, Jésus reprit: « Mes petits enfants, qu’il est difficile à ceux qui se confient dans les richesses, d’entrer dans le royaume de Dieu!
Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
25 Il est plus aisé à un chameau de passer par le trou d’une aiguille, qu’à un riche d’entrer dans le royaume de Dieu. »
Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
26 Et ils étaient encore plus étonnés, et ils se disaient les uns aux autres: « Qui peut donc être sauvé? »
Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
27 Jésus les regarda, et dit: « Aux hommes cela est impossible, mais non à Dieu: car tout est possible à Dieu. »
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
28 Alors Pierre, prenant la parole: « Voici, lui dit-il, que nous avons tout quitté pour te suivre. »
Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
29 Jésus répondit: « Je vous le dis en vérité, nul ne quittera sa maison, ou ses frères, ou ses sœurs, ou son père, ou sa mère, ou ses enfants, ou ses champs, à cause de moi et à cause de l’Evangile,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
30 qu’il ne reçoive maintenant, en ce temps présent, cent fois autant: maisons, frères, sœurs, mères, enfants et champs, au milieu même des persécutions, et dans le siècle à venir, la vie éternelle. (aiōn , aiōnios )
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn , aiōnios )
31 Et plusieurs des derniers seront les premiers, et des premiers, les derniers. »
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
32 Or, ils étaient en chemin pour monter à Jérusalem, et Jésus marchait devant eux; ils s’en étonnaient et ils le suivaient avec crainte. Jésus, de nouveau, prenant à part les Douze, se mit à leur dire ce qui devait lui arriver:
Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
33 « Voici que nous montons à Jérusalem, et le Fils de l’homme sera livré aux Princes des prêtres et aux scribes; ils le condamneront à mort et le livreront aux Gentils;
Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
34 on l’insultera, on crachera sur lui, on le flagellera et on le fera mourir, et, trois jours après, il ressuscitera. »
waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
35 Jacques et Jean, fils de Zébédée, s’approchèrent de lui, disant: « Maître, nous désirons bien que tu fasses pour nous ce que nous te demanderons.
Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
36 Que voulez-vous, leur dit-il, que je fasse pour vous? »
Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
37 Ils dirent: « Accorde-nous d’être assis, l’un à ta droite, l’autre à ta gauche, dans ta gloire. »
Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
38 Jésus leur dit: « Vous ne savez ce que vous demandez. Pouvez-vous boire la coupe que je vais boire, ou être baptisés du baptême dont je vais être baptisé? »
Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
39 Ils répondirent: « Nous le pouvons. » Et Jésus leur dit: « Le calice que je vais boire, vous le boirez en effet, et vous serez baptisés du baptême dont je vais être baptisé;
Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
40 mais d’être assis à ma droite ou à ma gauche, ce n’est pas à moi de l’accorder, si ce n’est à ceux à qui cela a été préparé. »
amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
41 Ayant entendu cela, les dix autres s’indignèrent contre Jacques et Jean.
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42 Jésus les appela et leur dit: « Vous savez que ceux qui sont reconnus comme les chefs des nations leur commandent en maîtres, et que les grands exercent sur elles l’empire.
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43 Il n’en doit pas être ainsi parmi vous; mais quiconque veut être grand parmi vous se fera votre serviteur;
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44 et quiconque veut être le premier parmi vous, se fera l’esclave de tous.
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45 Car le Fils de l’homme est venu, non pour être servi, mais pour servir et donner sa vie pour la rançon de la multitude. »
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
46 Ils arrivèrent à Jéricho. Comme Jésus sortait de cette ville avec ses disciples et une assez grande foule, le fils de Timée, Bartimée l’aveugle, était assis sur le bord du chemin, demandant l’aumône.
Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
47 Ayant entendu dire que c’était Jésus de Nazareth, il se mit à crier: « Jésus, fils de David, ayez pitié de moi. »
Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
48 Et plusieurs le réprimandait pour le faire taire; mais lui criait beaucoup plus fort: « Fils de David, aie pitié de moi. »
Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
49 Alors Jésus s’arrêta, et dit: « Appelez-le. » Et ils l’appelèrent en lui disant: « Aie confiance, lève-toi, il t’appelle. »
Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
50 Celui-ci jetant son manteau, se leva d’un bond et vint vers Jésus.
Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
51 Jésus lui dit: « Que veux-tu que je te fasse? – L’aveugle répondit: Rabbouni, que je voie. »
Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
52 Jésus lui dit: « Va, ta foi t’a sauvé. » Et aussitôt il vit, et il le suivait dans le chemin.
Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.