< Lamentations 1 >

1 Comment est-elle assise solitaire, la cité populeuse! Elle est devenue comme une veuve, celle qui était grande parmi les nations. Celle qui était reine parmi les provinces a été soumise au tribut.
Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
2 Elle pleure amèrement durant la nuit, et les larmes couvrent ses joues; pas un ne la console, de tous ses amants; tous ses compagnons l’ont trahie, ils sont devenus ses ennemis.
Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
3 Juda s’en est allé en exil, misérable et condamné à un rude travail; il habite chez les nations, sans trouver le repos; ses persécuteurs l’ont atteint dans d’étroits défilés.
Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
4 Les chemins de Sion sont dans le deuil, parce que nul ne vient plus à ses fêtes; Toutes ses portes sont en ruines, ses prêtres gémissent, ses vierges se désolent, et elle-même est dans l’amertume.
Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
5 Ses oppresseurs ont le dessus, ses ennemis prospèrent; car Yahweh l’a affligée, à cause de la multitude de ses offenses; ses petits enfants s’en sont allés captifs, devant l’oppresseur.
Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
6 Et la fille de Sion a perdu toute sa gloire; ses princes sont comme des cerfs qui ne trouvent pas de pâture, et qui s’en vont sans force devant celui qui les poursuit.
Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
7 Jérusalem se souvient, aux jours de son affliction et de sa vie errante, de tous ses biens précieux qu’elle possédait, dès les jours anciens. Maintenant que son peuple est tombé sous la main de l’oppresseur, et que personne ne vient a son aide, ses ennemis la voient, et ils rient de son chômage.
A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
8 Jérusalem a multiplié ses péchés; c’est pourquoi elle est devenue une chose souillée; tous ceux qui l’honoraient la méprisent, car ils ont vu sa nudité; elle-même pousse des gémissements, et détourne la face.
Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
9 Sa souillure apparaît sous les pans de sa robe; elle ne songeait pas à sa fin. Et elle est tombée d’une manière étrange, et personne ne la console! « Vois, Yahweh, ma misère, car l’ennemi triomphe! »
Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
10 L’oppresseur a étendu la main sur tous ses trésors; car elle a vu les nations entrer dans son sanctuaire, les nations au sujet desquelles tu avais donné cet ordre: « Elles n’entreront pas dans ton assemblée. »
Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
11 Tout son peuple gémit, cherchant du pain; ils donnent leurs joyaux pour des aliments, qui leur rendent la vie. « Vois Yahweh et considère l’abjection où je suis tombée! »
Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
12 « O vous tous, qui passez par le chemin, regardez et voyez s’il y a une douleur pareille à la douleur qui pèse sur moi, moi que Yahweh a frappée, au jour de son ardente colère!
“Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
13 « D’en haut il a lancé dans mes os un feu qui les dévore; il a étendu un filet devant mes pieds, il m’a fait reculer; il m’a jeté dans la désolation, je languis tout le jour.
“Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
14 « Le joug de mes iniquités a été lié dans sa main; unies en faisceau, elles pèsent sur mon cou; il a fait chanceler ma force. Le Seigneur m’a livré à des mains auxquelles je ne puis résister.
“Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
15 « Le Seigneur a enlevé tous les guerriers qui étaient au milieu de moi; il a appelé contre moi une armée, pour écraser mes jeunes hommes; le Seigneur a foulé au pressoir la vierge, fille de Juda.
“Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
16 « C’est pour cela que je pleure, que mon œil, mon œil se fond en larmes; car il n’y a près de moi personne qui me console, qui me rende la vie; mes fils sont dans la désolation, car l’ennemi l’emporte. »
“Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
17 Sion a tendu les mains... Personne qui la console! Yahweh a mandé contre Jacob ses ennemis qui l’enveloppent; Jérusalem est devenue au milieu d’eux comme une chose souillée.
Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
18 « Yahweh est vraiment juste, car j’ai été rebelle à ses ordres. Oh! écoutez tous, peuples, et voyez ma douleur: mes vierges et mes jeunes gens sont allés en exil!
“Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
19 J’ai appelé mes amants, ils m’ont trompée; mes prêtres et mes anciens ont péri dans la ville, en cherchant de la nourriture, pour ranimer leur vie.
“Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
20 « Regarde, Yahweh, quelle est mon angoisse! Mes entrailles sont émues; mon cœur est bouleversé au dedans de moi, parce que j’ai été bien rebelle. Au dehors l’épée tue mes enfants; au dedans, c’est la mort!
“Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
21 « On entend mes gémissements; personne qui me console! Tous mes ennemis, en apprenant mon malheur, se réjouissent de ce que tu as agi. Tu feras venir le jour que tu as annoncé, et ils deviendront tels que moi!
“Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
22 « Que toute leur méchanceté soit présente devant toi, pour que tu les traites comme tu m’as traitée moi-même, à cause de toutes mes offenses! Car mes gémissements sont nombreux, et mon cœur est malade! »
“Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”

< Lamentations 1 >