< Juges 5 >

1 En ce jour-là, Débora et Barac, fils d’Abinoëm, chantèrent en disant:
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
2 Les chefs se sont mis à la tête en Israël; le peuple s’est volontairement offert pour le combat, bénissez-en Yahweh!
“Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
3 Ecoutez, ô rois: princes, prêtez l’oreille. C’est moi, c’est moi qui chanterai Yahweh; je dirai un cantique à Yahweh, le Dieu d’Israël.
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
4 Yahweh, quand tu sortis de Séïr, quand tu t’avanças des campagnes d’Edom, la terre trembla, les cieux mêmes se fondirent, et les nuées se fondirent en eau.
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
5 Devant Yahweh s’ébranlèrent les montagnes, ce Sinaï, devant Yahweh, le Dieu d’Israël.
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
6 Aux jours de Samgar, fils d’Anath, aux jours de Jahel, les routes étaient désertes, et les voyageurs prenaient des sentiers détournés.
“A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
7 Les campagnes étaient dans l’abandon en Israël, jusqu’à ce que je me sois levée, moi Débora, que je me sois levée, une mère en Israël.
Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
8 On choisissait des dieux nouveaux; alors la guerre était aux portes, et l’on ne voyait ni bouclier ni lance chez quarante milliers en Israël!
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
9 Mon cœur s’élance vers les conducteurs d’Israël, vers ceux du peuple qui se sont offerts: Bénissez Yahweh!
Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
10 Vous qui montez de blanches ânesses, qui vous asseyez sur des tapis, et vous qui parcourez les chemins, chantez!
“Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
11 Que de leur voix les archers, près des abreuvoirs, célèbrent les justices de Yahweh, les justices envers ses campagnes en Israël! Alors le peuple de Yahweh est descendu dans ses portes.
da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
12 Eveille-toi, éveille-toi, Débora! Eveille-toi, éveille-toi, dis au cantique! Lève-toi, Barac, et fais tes prisonniers, fils d’Abinoëm!
‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
13 En ce moment descends, reste des nobles du peuple! Yahweh, descends vers moi parmi ces héros!
“Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
14 D’Ephraïm sont venus ceux qui ont leur racine en Amalec; derrière toi, Benjamin s’est joint à tes troupes; de Machir, des chefs sont descendus; de Zabulon des conducteurs, avec le bâton du scribe.
Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
15 Les princes d’Issachar sont avec Débora, Issachar est à côté de Barac; dans la plaine il est envoyé sur ses pas. Près des ruisseaux de Ruben, il y eut de grandes résolutions du cœur:
’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
16 Pourquoi es-tu resté au milieu de tes pâturages, à écouter le chalumeau de tes pâtres? Près des ruisseaux de Ruben, il y eut de grandes résolutions du cœur!
Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
17 Galaad n’a pas quitté sa demeure, au delà du Jourdain; et Dan, pourquoi s’est-il tenu dans ses vaisseaux? Aser est resté tranquille sur le rivage de la mer, et il est demeuré dans ses ports.
Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
18 Mais Zabulon est un peuple qui expose son âme à la mort, ainsi que Nephtali, sur ses hauts plateaux.
Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
19 Les rois sont venus, ils ont livré bataille; alors ils ont livré bataille, les rois de Canaan, à Thanac, au bord des eaux de Mageddo; ils n’ont pas remporté un seul lingot d’argent.
“Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
20 Du ciel on a combattu pour nous, de leurs sentiers les étoiles ont combattu contre Sisara.
Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
21 Le torrent de Cison a roulé leurs cadavres. le torrent des anciens temps, le torrent de Cison. — O mon âme, avance hardiment! —
Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
22 Alors retentirent les sabots des chevaux, dans la course, la course rapide de leurs guerriers.
Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
23 Maudissez Méroz, dit l’ange de Yahweh, maudissez, maudissez ses habitants! Car ils ne sont pas venus au secours de Yahweh, au secours de Yahweh, avec les vaillants.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
24 Bénie soit entre les femmes Jahel, femme de Héber, le Cinéen; entre les troupes qui habitent sous la tente bénie soit-elle!
“Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
25 Il demanda de l’eau, elle donna du lait; dans la coupe d’honneur, elle offrit le lait le plus pur.
Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
26 D’une main elle saisit le pieu, et de sa droite, le marteau de l’ouvrier. Elle frappe Sisara, elle lui brise la tête, elle fracasse et transperce sa tempe;
Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
27 à ses pieds, il s’affaisse, il tombe, il est étendu; à ses pieds il s’affaisse, il tombe: là où il s’affaisse, là il gît inanimé.
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
28 Par la fenêtre, à travers le treillis, elle regarde, la mère de Sisara, et pousse des cris: « Pourquoi son char tarde-t-il à venir? Pourquoi est-elle si lente la marche de ses chariots? »
“Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
29 Les plus avisées de ses dames lui répondent, et elle se répète à elle-même leurs paroles:
Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
30 « N’ont-ils pas trouvé, ne se partagent-ils pas le butin? Une jeune fille, deux jeunes filles pour chaque guerrier; des vêtements de couleur pour butin à Sisara, des vêtements de couleur variée pour butin; un vêtement de couleur, deux vêtements de couleur variée, pour les épaules de l’épouse! »
‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
31 Qu’ainsi périssent tous tes ennemis, ô Yahweh! Et que ceux qui l’aiment soient comme le soleil, quand il se lève dans sa force! Le pays fut en repos pendant quarante ans.
“Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.

< Juges 5 >