< Juges 3 >
1 Voici les nations que Yahweh laissa en repos pour éprouver par elles Israël, tous ceux qui n’avaient pas connu toutes les guerres de Canaan,
Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
2 et cela uniquement pour l’instruction des générations d’Israël, afin de leur apprendre la guerre, à ceux-là du moins qui ne l’avaient pas connue auparavant.
(ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
3 Ces nations étaient: les cinq princes des Philistins, tous les Chananéens et les Sidoniens, et les Hévéens qui habitaient la montagne du Liban, depuis la montagne de Baal-Hermon jusqu’à l’entrée de Hamath.
sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
4 Ces peuples devaient servir à mettre Israël à l’épreuve, pour savoir s’ils obéiraient aux commandements que Yahweh avait prescrits à leurs pères par Moïse.
An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
5 Et les enfants d’Israël habitèrent au milieu des Chananéens, des Hittites, des Amorrhéens, des Phérézéens, des Hévéens et des Jébuséens;
Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
6 ils prirent leurs filles pour femmes, et donnèrent à leurs fils leurs propres filles, et ils servirent leurs dieux.
Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
7 Les enfants d’Israël firent ce qui est mal aux yeux de Yahweh; oubliant Yahweh, ils servirent les Baals et les Aschéroth.
Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
8 La colère de Yahweh s’enflamma contre Israël, et il les vendit entre les mains de Chusan-Rasathaïm, roi de Mésopotamie, et les enfants d’Israël furent asservis huit ans à Chusan-Rasathaïm.
Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
9 Les enfants d’Israël, crièrent vers Yahweh, et Yahweh leur suscita un libérateur qui les délivra, Othoniel, fils de Cènez, frère cadet de Caleb.
Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
10 L’Esprit de Yahweh vint sur lui; il jugea Israël et partit pour la guerre; Yahweh livra entre ses mains Chusan-Rasathaïm, roi de Mésopotamie, et sa main fut puissante contre Chusan-Rasathaïm.
Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
11 Le pays fut en repos pendant quarante ans, et Othoniel, fils de Cénez, mourut.
Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
12 Les enfants d’Israël firent de nouveau ce qui est mal aux yeux de Yahweh, et Yahweh fortifia Eglon, roi de Moab, contre Israël, parce qu’ils faisaient ce qui est mal aux yeux de Yahweh.
Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
13 Eglon s’adjoignit les fils d’Ammon et Amalec, et il se mit en marche. Il battit Israël, et ils s’emparèrent de la ville des Palmiers.
Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
14 Les enfants d’Israël furent asservis dix-huit ans à Eglon, roi de Moab.
Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
15 Les enfants d’Israël crièrent vers Yahweh, et Yahweh leur suscita un libérateur, Aod, fils de Géra, Benjamite, qui ne se servait pas de la main droite. Les enfants d’Israël envoyèrent par lui un présent à Eglon, roi de Moab.
Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
16 Aod se fit une épée à deux tranchants, longue d’une coudée, et il la ceignit sous ses vêtements, sur sa hanche droite.
To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
17 Il offrit le Présent à Eglon. roi de Moab; or Eglon était un homme très gras.
Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
18 Lorsqu’il eut achevé d’offrir le présent, il renvoya les gens qui avaient apporté le présent.
Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
19 Et lui-même revint depuis les idoles qui sont près de Galgala, et il dit: « O roi, j’ai quelque chose de secret à te dire. » Le roi dit: « Silence! » Et tous ceux qui étaient auprès de lui sortirent.
A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
20 Aod l’aborda comme il était assis seul dans sa chambre d’été, et il dit: « J’ai pour toi une parole de Dieu. » Eglon se leva de son siège.
Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
21 Alors Aod, avançant la main gauche, tira l’épée qui était sur sa hanche droite, et la lui enfonça dans le ventre.
Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
22 La poignée même entra après la lame, et la graisse se referma sur la lame; car il ne retira pas l’épée de son ventre, et la lame sortit par derrière.
Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
23 Aod sortit par l’escalier extérieur, ferma sur Eglon les portes de la chambre haute et tira le verrou.
Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
24 Quand il fut sorti, les serviteurs du roi vinrent et regardèrent; et voici que les portes de la chambre haute étaient fermées au verrou. Ils dirent: « Sans doute il se couvre les pieds dans la chambre d’été. »
Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
25 Ils attendirent longtemps jusqu’à en avoir honte, et, comme il n’ouvrait pas les portes de la chambre haute, ils prirent la clef et ouvrirent; et voici que leur maître gisait par terre, sans vie.
Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
26 Pendant leurs délais, Aod prit la fuite, dépassa les idoles et se sauva à Séïrath.
Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
27 Aussitôt arrivé, il sonna de la trompette dans la montagne d’Ephraïm. Les enfants d’Israël descendirent avec lui de la montagne, et il se mit à leur tête.
Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
28 Il leur dit: « Suivez-moi! car Yahweh a livré entre vos mains vos ennemis, les Moabites. » Ils descendirent à sa suite, s’emparèrent des gués du Jourdain vis-à-vis de Moab, et ne laissèrent passer personne.
Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
29 Ils battirent Moab en ce temps-là, environ dix mille hommes, tous robustes et tous vaillants, et pas un n’échappa.
A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
30 En ce jour, Moab fut humilié sous la main d’Israël, et le pays fut en repos pendant quatre-vingt ans.
A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
31 Après lui, il y eut Samgar, fils d’Anath, qui battit six cents hommes des Philistins avec un aiguillon à bœufs; lui aussi fut un libérateur d’Israël.
Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.