< Juges 21 >
1 Les hommes d’Israël avaient juré à Maspha, en disant: « Aucun de nous ne donnera sa fille pour femme à un Benjamite. »
Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
2 Le peuple vint à Béthel, et il y resta devant Dieu jusqu’au soir. Elevant la voix, ils firent de grandes lamentations, et ils dirent:
Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
3 « Pourquoi, ô Yahweh, Dieu d’Israël, est-il arrivé en Israël qu’il manque aujourd’hui une tribu d’Israël? »
Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
4 Le lendemain, le peuple s’étant levé dès le matin, ils bâtirent là un autel, et ils offrirent des holocaustes et des sacrifices pacifiques.
Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
5 Et les enfants d’Israël dirent: « Quel est celui d’entre toutes les tribus d’Israël qui n’est pas monté à l’assemblée devant Yahweh? » Car on avait fait un serment solennel contre celui qui ne monterait pas vers Yahweh à Maspha, en disant: « Il sera puni de mort. »
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
6 Les enfants d’Israël avaient compassion de Benjamin, leur frère, et ils disaient: « Une tribu a été retranchée aujourd’hui d’Israël!
To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
7 Que ferons-nous pour eux, pour procurer des femmes à ceux qui restent? Car nous avons juré par Yahweh de ne pas leur donner de nos filles pour femmes »
Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
8 Ils dirent donc: « Y a-t-il une seule d’entre les tribus d’Israël qui ne soit pas montée vers Yahweh à Maspha? » Et voici, personne de Jabès en Galaad n’était venu au camp, à l’assemblée.
Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
9 On fit le recensement du peuple, et voici qu’il n’y avait là aucun des habitants de Jabès en Galaad.
Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
10 Alors l’assemblée envoya contre eux douze mille hommes d’entre les vaillants, en leur donnant cet ordre: « Allez, et frappez du tranchant de l’épée les habitants de Jabès en Galaad, avec les femmes et les enfants.
Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
11 Voici ce que vous ferez: vous dévouerez à l’anathème tout homme, et toute femme qui a connu la couche d’un homme. »
Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
12 Ils trouvèrent parmi les habitants de Jabès en Galaad quatre cents jeunes filles vierges, qui n’avaient pas connu d’homme en partageant sa couche, et ils les amenèrent dans le camp à Silo, qui est au pays de Canaan.
Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
13 Alors toute l’assemblée envoya des messagers pour parler aux fils de Benjamin qui étaient réfugiés au rocher de Remmon, et pour leur annoncer la paix.
Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
14 Les Benjamites revinrent en ce temps-là, et on leur donna les femmes à qui on avait laissé la vie parmi les femmes de Jabès en Galaad; mais il ne s’en trouva pas assez pour eux.
Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
15 Le peuple avait compassion de Benjamin, car Yahweh avait fait une brèche dans les tribus d’Israël.
Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
16 Les anciens de l’assemblée dirent: « Que ferons-nous pour procurer des femmes à ceux qui restent, puisque les femmes de Benjamin ont été détruites? »
Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
17 Et ils dirent: « Que l’héritage de ceux qui ont échappé demeure à Benjamin, afin qu’une tribu ne soit pas effacée d’Israël.
Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
18 Mais nous, nous ne pouvons pas leur donner de nos filles pour femmes, car les enfants d’Israël ont juré, en disant: « Maudit soit celui qui donnera sa fille pour femme à un Benjamite? »
Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
19 Et ils dirent: « Voici une fête de Yahweh, qui se célèbre chaque année à Silo, ville située au nord de Béthel, à l’orient de la route qui monte de Béthel à Sichem, et au midi de Lébona. »
Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
20 Puis ils donnèrent cet ordre aux fils de Benjamin: « Allez, et placez-vous en embuscade dans les vignes.
Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
21 Vous regarderez, et, lorsque les filles de Silo sortiront pour danser en chœur, vous sortirez des vignes, et vous enlèverez chacun votre femme d’entre les filles de Silo, et vous vous en irez dans le pays de Benjamin.
ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
22 Si leurs pères ou leurs frères viennent réclamer auprès de nous, nous leur dirons: Laissez-les-nous, car nous n’avons pas pris une femme pour chacun dans la guerre. Et ce n’est pas vous qui les leur avez données; en ce cas, vous seriez coupables. »
Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
23 Les fils de Benjamin firent ainsi: ils prirent des femmes selon leur nombre parmi les danseuses, qu’ils enlevèrent, et, s’étant mis en route, ils retournèrent dans leur héritage; ils rebâtirent les villes et ils y habitèrent.
Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
24 En ce temps-là, les enfants d’Israël s’en allèrent de là, chacun dans sa tribu et dans sa famille, et ils retournèrent de là, chacun dans son héritage.
A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
25 En ces jours-là, il n’y avait pas de roi en Israël; chacun faisait ce qui était bon...
A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.