< Juges 10 >

1 Après Abimélek, Thola, fils de Phua, fils de Dodo, homme d’Issachar, se leva pour délivrer Israël; il demeurait à Samir, dans la montagne d’Ephraïm.
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 Il fut juge en Israël pendant vingt-trois ans; puis il mourut et fut enterré à Samir.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 Après lui se leva Jaïr, de Galaad, qui jugea Israël pendant vingt-deux ans.
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 Il avait trente fils, qui montaient trente ânons, et qui possédaient trente villes appelées encore aujourd’hui Bourgs de Jaïr, et situées dans le pays de Galaad.
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 Et Jaïr mourut, et il fut enterré à Camon.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 Les enfants d’Israël firent encore ce qui est mal aux yeux de Yahweh; ils servirent les Baals et les Astartés, les dieux de Syrie, les dieux de Sidon, les dieux de Moab, les dieux des fils d’Ammon et les dieux des Philistins, et ils abandonnèrent Yahweh et ne le servirent plus.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 La colère de Yahweh s’enflamma contre Israël, et il les vendit entre les mains des Philistins et entre les mains des fils d’Ammon.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 Ces derniers opprimèrent et écrasèrent les enfants d’Israël en cette année-là; et cette oppression dura dix-huit ans pour tous les enfants d’Israël qui habitaient de l’autre côté du Jourdain, dans le pays des Amorrhéens en Galaad.
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 Les fils d’Ammon passèrent le Jourdain pour combattre aussi Juda, Benjamin et la maison d’Ephraïm; et Israël fut réduit à une grande détresse.
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 Les enfants d’Israël crièrent vers Yahweh, en disant: « Nous avons péché contre vous, car nous avons abandonné notre Dieu et nous avons servi les Baals. »
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 Yahweh dit aux enfants d’Israël: « Est-ce que je ne vous ai pas délivrés des Egyptiens, des Amorrhéens, des fils d’Ammon, des Philistins?
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 Et lorsque les Sidoniens, Amalec et Maon vous ont opprimés, et que vous avez crié vers moi, ne vous ai-je pas sauvés de leurs mains?
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 Mais vous, vous m’avez abandonné et vous avez servi d’autres dieux; c’est pourquoi je ne vous délivrerai plus.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Allez, invoquez les dieux que vous vous êtes choisis; qu’ils vous délivrent au temps de votre détresse! »
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 Les enfants d’Israël dirent à Yahweh: « Nous avons péché, traitez-nous tous comme il vous semblera bon. Seulement daignez nous délivrer en ce jour. »
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 Et ils ôtèrent du milieu d’eux les dieux étrangers, et ils servirent Yahweh, et son âme ne put supporter les souffrances d’Israël.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 Les fils d’Ammon se rassemblèrent et campèrent en Galaad, et les enfants d’Israël se réunirent et campèrent à Maspha.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 Le peuple, les chefs de Galaad se dirent les uns aux autres: « Quel est l’homme qui commencera l’attaque contre les fils d’Ammon? Il deviendra chef de tous les habitants de Galaad. »
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”

< Juges 10 >