< Josué 23 >

1 Un long temps s’était écoulé depuis que Yahweh avait donné du repos à Israël, en le délivrant de tous ses ennemis d’alentour, et Josué était vieux, avancé en âge.
An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
2 Alors Josué convoqua tout Israël, ses anciens, ses chefs, ses juges et ses officiers, et leur dit: « Je suis devenu vieux, avancé en âge.
sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
3 Vous avez vu tout ce que Yahweh, votre Dieu a fait à toutes ces nations devant vous; car c’est Yahweh, votre Dieu, qui a combattu pour vous.
ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
4 Voyez: je vous ai distribué par le sort en héritage pour vos tribus, ces nations qui sont restées et toutes celles que j’ai exterminées, depuis le Jourdain jusqu’à la grande mer vers le soleil couchant.
Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
5 Yahweh, votre Dieu, les repoussera devant vous, et les chassera devant vous, et vous posséderez leur pays, comme Yahweh, votre Dieu, vous l’a dit.
Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
6 Montrez donc un grand courage pour observer et mettre en pratique tout ce qui est écrit dans le livre de la loi de Moïse, sans vous en détourner ni à droite ni à gauche,
“Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
7 sans vous mêler avec ces nations qui sont restées parmi vous; n’invoquez pas le nom de leurs dieux, ne jurez pas par eux, ne les servez pas et ne vous prosternez pas devant eux;
Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
8 mais attachez-vous à Yahweh, votre Dieu, comme vous l’avez fait jusqu’à ce jour.
Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
9 Yahweh a chassé devant vous des nations grandes et puissantes, et personne n’a pu tenir devant vous jusqu’à ce jour.
“Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
10 Un seul d’entre vous en poursuivait mille, car Yahweh, votre Dieu, combattait pour vous, comme il vous l’a dit.
Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
11 Prenez donc garde à vous mêmes, pour que vous aimiez Yahweh, votre Dieu.
Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
12 Car si vous vous détournez et que vous vous attachiez au reste de ces nations qui sont demeurées parmi vous, si vous contractez des mariages avec elles et que vous vous mêliez à elles et qu’elles se mêlent à vous,
“Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
13 sachez bien que Yahweh, votre Dieu, ne continuera pas de chasser ces nations devant nous; mais elles seront pour vous un filet et un piège, une verge sur vos flancs et des épines dans vos yeux, jusqu’à ce que vous ayez péri de dessus cette excellente terre que vous a donnée Yahweh, votre Dieu.
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
14 Voici que je m’en vais aujourd’hui par le chemin de toute la terre; reconnaissez de tout votre cœur et de toute votre âme, que, de toutes les bonnes paroles que Yahweh, votre Dieu, a prononcées sur vous, aucune parole n’est restée sans effet; toutes se sont accomplies pour vous, aucune parole n’en est tombée.
“Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
15 De même donc que toutes les bonnes paroles que Yahweh, votre Dieu, vous a adressées, se sont accomplies pour vous, de même aussi Yahweh accomplira sur vous toutes les paroles de menace, jusqu’à ce qu’il vous ait détruits de dessus cette excellente terre que Yahweh, votre Dieu, vous a donnée.
Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
16 Si vous transgressez l’alliance de Yahweh, votre Dieu, qu’il vous a prescrite, et si vous allez servir d’autres dieux, et vous prosterner devant eux, la colère de Yahweh s’enflammera contre vous, et vous périrez bientôt de dessus le bon pays qu’il vous a donné. »
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”

< Josué 23 >