< Job 7 >
1 La vie de l’homme sur la terre est un temps de service, et ses jours sont comme ceux du mercenaire.
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Comme l’esclave soupire après l’ombre, comme l’ouvrier attend son salaire,
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 ainsi j’ai eu en partage des mois de douleur, pour mon lot, des nuits de souffrance.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 Si je me couche, je dis: « Quand me lèverai-je? Quand finira la nuit? » et je suis rassasié d’angoisses jusqu’au jour.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 Ma chair se couvre de vers et d’une croûte terreuse, ma peau se gerce et coule.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 Mes jours passent plus rapides que la navette, ils s’évanouissent: plus d’espérance!
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 O Dieu, souviens-toi que ma vie n’est qu’un souffle! Mes yeux ne reverront pas le bonheur.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 L’œil qui me regarde ne m’apercevra plus; ton œil me cherchera, et je ne serai plus.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 Le nuage se dissipe et passe; ainsi celui qui descend au schéol ne remontera plus; (Sheol )
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
10 il ne retournera plus dans sa maison; le lieu qu’il habitait ne le reconnaîtra plus.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 C’est pourquoi je ne retiendrai pas ma langue, je parlerai dans l’angoisse de mon esprit, j’exhalerai mes plaintes dans l’amertume de mon âme.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Suis-je la mer ou un monstre marin, pour que tu poses une barrière autour de moi?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 Quand je dis: « Mon lit me soulagera, ma couche calmera mes soupirs, »
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 alors tu m’effraies par des songes, tu m’épouvantes par des visions.
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 Ah! Mon âme préfère la mort violente, mes os appellent le trépas.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 Je suis en proie à la dissolution, la vie m’échappe pour jamais; laisse-moi, car mes jours ne sont qu’un souffle.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 Qu’est-ce que l’homme, pour que tu en fasses tant d’estime, que tu daignes t’occuper de lui,
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 que tu le visites chaque matin, et qu’à chaque instant tu l’éprouves?
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Quand cesseras-ru d’avoir le regard sur moi? Quand me laisseras-tu le temps d’avaler ma salive?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 Si j’ai péché, que puis-je te faire, ô Gardien des hommes? Pourquoi me mettre en butte à tes traits, et me rendre à charge à moi-même?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 Que ne pardonnes-tu mon offense? Que n’oublies-tu mon iniquité? Car bientôt je dormirai dans la poussière; tu me chercheras, et je ne serai plus.
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”