< Job 35 >

1 Eliu prit de nouveau la parole et dit:
Sai Elihu ya ce,
2 Crois-tu que ce soit là de la justice, de dire: « J’ai raison contre Dieu? »
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 Car tu as dit: « Que me sert mon innocence, qu’ai-je de plus que si j’avais péché? »
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Moi, je vais te répondre, et à tes amis en même temps.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Considère les cieux et regarde; vois les nuées: elles sont plus hautes que toi!...
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 Si tu pèches, quel tort lui causes-tu? Si tes offenses se multiplient, que lui fais-tu?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Si tu es juste, que lui donnes-tu? Que reçoit-il de ta main?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Ton iniquité ne peut nuire qu’à tes semblables, ta justice n’est utile qu’au fils de l’homme.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 Des malheureux gémissent sous la violence des vexations, et crient sous la main des puissants.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Mais nul ne dit: « Où est Dieu, mon Créateur, qui donne à la nuit des chants de joie,
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 qui nous a faits plus intelligents que les animaux de la terre, plus sages que les oiseaux du ciel. »
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 Ils crient alors, sans être exaucés, sous l’orgueilleuse tyrannie des méchants.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Dieu n’exauce pas les discours insensés, le Tout-Puissant ne les regarde pas.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Quand tu lui dis: « Tu ne vois pas ce qui se passe, » ta cause est devant lui; attends son jugement.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 Mais, parce que sa colère ne sévit pas encore, et qu’il semble ignorer sa folie,
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Job prête sa bouche à de vaines paroles, et se répand en discours insensés.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”

< Job 35 >