< Job 28 >
1 Il y a pour l’argent un lieu d’où on l’extrait, pour l’or un lieu où on l’épure.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Le fer se tire de la terre, et la pierre fondue donne le cuivre.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 L’homme met fin aux ténèbres, il explore, jusqu’au fond des abîmes, la pierre cachée dans les ténèbres et l’ombre de la mort.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 Il creuse, loin des lieux habités, des galeries, qu’ignore le pied des vivants; suspendu, il vacille, loin des humains.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 La terre, d’où sort le pain, est bouleversée dans ses entrailles comme par le feu.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Ses roches sont le lieu du saphir, et l’on y trouve de la poudre d’or.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 L’oiseau de proie n’en connaît pas le sentier, l’œil du vautour ne l’a pas aperçu.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 Les animaux sauvages ne l’ont pas foulé, le lion n’y a jamais passé.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 L’homme porte sa main sur le granit, il ébranle les montagnes dans leurs racines.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 Il perce des galeries dans les rochers; rien de précieux n’échappe à son regard.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 Il sait arrêter le suintement des eaux, il amène à la lumière tout ce qui était caché.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 Mais la Sagesse, où la trouver? Où est le lieu de l’Intelligence?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 L’homme n’en connaît pas le prix, on ne la rencontre pas sur la terre des vivants.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 L’abîme dit: « Elle n’est pas dans mon sein; » la mer dit: « Elle n’est pas avec moi. »
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Elle ne se donne pas contre de l’or pur, elle ne s’achète pas au poids de l’argent.
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 On ne la met pas en balance avec de l’or d’Ophir, avec l’onyx précieux et avec le saphir.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 L’or et le verre ne peuvent lui être comparés, on ne l’échange pas pour un vase d’or fin.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 Qu’on ne fasse pas mention du corail et du cristal: la possession de la sagesse vaut mieux que les perles.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 La topaze d’Ethiopie ne l’égale pas, et l’or pur n’atteint pas sa valeur.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 D’où vient donc la sagesse? Où est lieu de l’Intelligence?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 Elle est cachée aux yeux de tous les vivants, elle se dérobe aux oiseaux du ciel.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 L’enfer et la mort disent: « Nous en avons entendu parler. » ()
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 C’est Dieu qui connaît son chemin, c’est lui qui sait où elle réside.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 Car il voit jusqu’aux extrémités de la terre, il aperçoit tout ce qui est sous le ciel.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Quand il réglait le poids des vents, qu’il mettait les eaux dans la balance,
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 quand il donnait des lois à la pluie, qu’il traçait la route aux éclairs de la foudre,
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 alors il l’a vue et l’a décrite, il l’a établie et en a sondé les secrets.
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 Puis il a dit à l’homme: La crainte du Seigneur, voilà la sagesse; fuir le mal, voilà l’intelligence.
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”