< Job 22 >

1 Alors Eliphaz prit la parole et dit:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 L’homme peut-il être utile à Dieu? Le sage n’est utile qu’à lui-même.
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Qu’importe au Tout-Puissant que tu sois juste? Si tu es intègre dans tes voies, qu’y gagne-t-il?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Est-ce à cause de ta piété qu’il te châtie, qu’il entre en jugement avec toi?
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Ta malice n’est-elle pas immense, tes iniquités sans mesure?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Tu prenais sans motif des gages à tes frères, tu enlevais les vêtements à ceux qui étaient nus.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Tu ne donnais pas d’eau à l’homme épuisé, à l’affamé tu refusais le pain.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 La terre était au bras le plus fort, et le protégé y établissait sa demeure.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Tu renvoyais les veuves les mains vides, et les bras des orphelins étaient brisés.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Voilà pourquoi tu es entouré de pièges, et troublé par des terreurs soudaines,
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 au sein des ténèbres, sans voir, et submergé par le déluge des eaux.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Dieu n’est-il pas dans les hauteurs du ciel? Vois le front des étoiles: comme il est élevé!
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Et tu disais: « Qu’en sait Dieu? Pourra-t-il juger à travers les nues profondes?
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Les nues lui forment un voile, et il ne voit pas; il se promène sur le cercle du ciel. »
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Gardes-tu donc les voies anciennes, où marchèrent les hommes d’iniquité,
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 qui furent emportés avant le temps, dont les fondements ont été arrachés par les eaux.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Eux qui disaient à Dieu: « Retire-toi de nous! Que pourrait nous faire le Tout-Puissant? »
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 C’était lui pourtant qui avait rempli leurs maisons de richesses. — Loin de moi le conseil des méchants! —
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Les justes voient leur chute et s’en réjouissent; les innocents se moquent d’eux:
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 « Voilà nos ennemis anéantis! Le feu a dévoré leurs richesses! »
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Réconcilie-toi donc avec Dieu et apaise-toi; ainsi le bonheur te sera rendu.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Reçois de sa bouche l’enseignement, et mets ses paroles dans ton cœur.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Tu te relèveras, si tu reviens au Tout-Puissant, si tu éloignes l’iniquité de ta tente.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 Jette les lingots d’or dans la poussière, et l’or d’Ophir parmi les cailloux du torrent.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 Et le Tout-Puissant sera ton or, il sera pour toi un monceau d’argent.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Alors tu mettras tes délices dans le Tout-Puissant, et tu lèveras vers lui ta face.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Tu le prieras, et il t’écoutera, et tu t’acquitteras de tes vœux.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Si tu formes un dessein, il te réussira, sur tes sentiers brillera la lumière.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 A des fronts abattus tu crieras: « En haut! » et Dieu secourra celui dont les yeux sont abaissés.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Il délivrera même le coupable, sauvé par la pureté de tes mains.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Job 22 >