< Job 21 >
1 Alors Job prit la parole et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Ecoutez, écoutez mes paroles, que j’aie, du moins, cette consolation de vous.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Permettez-moi de parler à mon tour, et, quand j’aurai parlé, vous pourrez vous moquer.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Est-ce contre un homme que se porte ma plainte? Comment donc la patience ne m’échapperait elle pas?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Regardez-moi et soyez dans la stupeur, et mettez la main sur votre bouche.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Quand j’y pense, je frémis; et un frissonnement saisit ma chair.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Pourquoi les méchants vivent-ils, et vieillissent-ils, accroissant leur force?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Leur postérité s’affermit autour d’eux, leurs rejetons fleurissent à leurs yeux.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Leur maison est en paix, à l’abri de la crainte; la verge de Dieu ne les touche pas.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Leur taureau est toujours fécond, leur génisse enfante et n’avorte pas.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Ils laissent courir leurs enfants comme un troupeau, leurs nouveau-nés bondissent autour d’eux.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Ils chantent au son du tambourin et de la cithare, ils se divertissent au son du chalumeau.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ils passent leurs jours dans le bonheur, et ils descendent en un instant au schéol. (Sheol )
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
14 Pourtant ils disaient à Dieu: « Retire-toi de nous; nous ne désirons pas connaître tes voies.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Qu’est-ce que le Tout-Puissant, pour que nous le servions? Que gagnerions-nous à le prier? »
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Leur prospérité n’est-elle pas dans leur main? — Toutefois, loin de moi le conseil de l’impie! —
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Voit-on souvent s’éteindre la lampe des impies, la ruine fondre sur eux, et Dieu leur assigner un lot dans sa colère?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Les voit-on comme la paille emportée par le vent, comme la glume enlevée par le tourbillon?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 « Dieu, dites-vous, réserve à ses enfants son châtiment!... » Mais que Dieu le punisse lui-même pour qu’il le sente,
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 qu’il voie de ses yeux sa ruine, qu’il boive lui-même la colère du Tout-Puissant!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Que lui importe, en effet, sa maison après lui, une fois que le nombre de ses mois est tranché?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Est-ce à Dieu qu’on apprendra la sagesse, à lui qui juge les êtres les plus élevés?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 L’un meurt au sein de sa prospérité, parfaitement heureux et tranquille,
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 les flancs chargés de graisse, et la mœlle des os remplie de sève.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 L’autre meurt, l’amertume dans l’âme, sans avoir goûté le bonheur.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Tous deux se couchent également dans la poussière, et les vers les couvrent tous deux.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Ah! Je sais bien quelles sont vos pensées, quels jugements iniques vous portez sur moi.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Vous dites: « Où est la maison de l’oppresseur! Qu’est devenue la tente qu’habitaient les impies? »
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 N’avez-vous donc jamais interrogé les voyageurs, et ignorez-vous leurs remarques?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 Au jour du malheur, le méchant est épargné; au jour de la colère, il échappe au châtiment.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Qui blâme devant lui sa conduite? Qui lui demande compte de ce qu’il a fait?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 On le porte honorablement au tombeau; et on veille sur son mausolée.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 les glèbes de la vallée lui sont légères, et tous les hommes y vont à sa suite, comme des générations sans nombre l’y ont précédé.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Que signifient donc vos vaines consolations? De vos réponses il ne reste que perfidie.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”