< Job 18 >

1 Alors Baldad de Suhé prit la parole et dit:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Quand donc mettrez-vous un terme à ces discours? Ayez de l’intelligence, puis nous parlerons.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Pourquoi nous regardez-vous comme des brutes, et sommes-nous stupides à vos yeux?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Toi qui te déchires dans ta fureur, veux-tu qu’à cause de toi la terre devienne déserte, que le rocher soit transporté hors de sa place?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Oui, la lumière du méchant s’éteindra, et la flamme de son foyer cessera de briller.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 Le jour s’obscurcira sous sa tente, sa lampe s’éteindra au-dessus de lui.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Ses pas si fermes seront à l’étroit, son propre conseil précipite sa chute.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Ses pieds le jettent dans les rets, il marche sur le piège.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Le filet saisit ses talons; il est serré dans ses nœuds.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Pour lui les lacs sont cachés sous terre, et la trappe est sur son sentier.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 De tous côtés des terreurs l’assiègent, et le poursuivent pas à pas.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 La disette est son châtiment, et la ruine est prête pour sa chute.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 La peau de ses membres est dévorée; ses membres sont dévorés par le premier-né de la mort.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Il est arraché de sa tente, où il se croyait en sûreté; on le traîne vers le Roi des frayeurs.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Nul des siens n’habite dans sa tente, le soufre est semé sur sa demeure.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 En bas, ses racines se dessèchent, en haut, ses rameaux sont coupés.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Sa mémoire a disparu de la terre, il n’a plus de nom dans la contrée.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 On le chasse de la lumière dans les ténèbres, on le bannit de l’univers.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Il ne laisse ni descendance ni postérité dans sa tribu; aucun survivant dans son séjour.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Les peuples de l’Occident sont stupéfaits de sa ruine, et ceux de l’Orient en sont saisis d’horreur.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Telle est la demeure de l’impie, telle est la place de l’homme qui ne connaît pas Dieu.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >