< Job 10 >
1 Mon âme est lasse de la vie; je donnerai libre cours à ma plainte, je parlerai dans l’amertume de mon cœur.
“Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
2 Je dis à Dieu: Ne me condamne point; apprends-moi sur quoi tu me prends à partie.
Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
3 Trouves-tu du plaisir à opprimer, à repousser l’œuvre de tes mains, à faire luire ta faveur sur le conseil des méchants?
Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
4 As-tu des yeux de chair, ou bien vois-tu comme voient les hommes?
Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
5 Tes jours sont-ils comme les jours de l’homme, ou bien tes années comme les années d’un mortel,
Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
6 pour que tu recherches mon iniquité, pour que tu poursuives mon péché,
da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
7 quand tu sais que je ne suis pas coupable, et que nul ne peut me délivrer de ta main?
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
8 Tes mains m’ont formé et façonné, tout entier, et tu voudrais me détruire!
“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
9 Souviens-toi que tu m’as pétri comme l’argile: et tu me ramènerais à la poussière!
Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
10 Ne m’as-tu pas coulé comme le lait, et coagulé comme le fromage?
Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
11 Tu m’as revêtu de peau et de chair, tu m’as tissé d’os et de nerfs.
Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
12 Avec la vie, tu m’as accordé ta faveur, et ta providence a gardé mon âme.
Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
13 Et pourtant, voilà ce que tu cachais dans ton cœur: Je vois bien ce que tu méditais.
“Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
14 Si je pèche, tu m’observes, tu ne me pardonnes pas mon iniquité.
In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
15 Suis-je coupable, malheur à moi! Suis-je innocent, je n’ose lever la tête, rassasié de honte, et voyant ma misère.
Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
16 Si je me relève, tu me poursuis comme un lion, tu recommences à me tourmenter étrangement,
In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
17 tu m’opposes de nouveaux témoins; tu redoubles de fureur contre moi, des troupes de rechange viennent m’assaillir.
Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
18 Pourquoi m’as-tu tiré du sein de ma mère? Je serais mort, et aucun œil ne m’aurait vu.
“Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
19 Je serais comme si je n’eusse jamais été, du sein maternel j’aurais été porté au sépulcre.
Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
20 Mes jours ne sont-ils pas bien courts? Qu’il me laisse! Qu’il se retire et que je respire un instant,
’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
21 avant que je m’en aille, pour ne plus revenir, dans la région des ténèbres et de l’ombre de la mort,
kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
22 morne et sombre région, où règnent l’ombre de la mort et le chaos, où la clarté est pareille aux ténèbres.
zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”