< Jérémie 25 >

1 La parole qui fut adressée à Jérémie touchant tout le peuple de Juda, en la quatrième année de Joakim, fils de Josias, roi de Juda, — c’était la première année de Nabuchodonosor, roi de Babylone —;
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 parole que Jérémie prononça sur tout le peuple de Juda et pour tous les habitants de Jérusalem, en ces termes:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 Depuis la treizième année de Josias, fils d’Amon, roi de Juda, jusqu’à ce jour, voici vingt-trois ans que la parole de Yahweh m’a été adressée et que je vous ai parlé, vous parlant dès le matin, et que vous n’avez pas écouté!
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 Yahweh vous a envoyé tous ses serviteurs les prophètes, les envoyant dès le matin, et vous n’avez pas écouté, et vous n’avez pas prêté l’oreille pour entendre.
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 Il disait: « Revenez-donc chacun de votre mauvaise voie et de la perversité de vos actions, et vous habiterez dans le pays que Yahweh a donné à vous et à vos pères, d’âge en âge.
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 N’allez pas après d’autres dieux pour les servir et les adorer; ne m’irritez pas par l’ouvrage de vos mains, et je ne vous ferai aucun mal.
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 Mais vous ne m’avez pas écouté, — oracle de Yahweh, — afin de m’irriter par l’œuvre de vos mains, pour votre malheur.
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 C’est pourquoi ainsi parle Yahweh des armées: Parce que vous n’avez pas écouté mes paroles,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 voici que j’envoie prendre toutes les tribus du septentrion, — oracle de Yahweh, — et je les amène à Nabuchodonosor, roi de Babylone, mon serviteur; je les ferai venir contre ce pays et contre ses habitants, et contre toutes ces nations d’alentour, que je frapperai d’anathème, et dont je ferai une solitude, un objet de moquerie, une ruine éternelle.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 Je ferai disparaître du milieu d’eux les cris de joie et les cris d’allégresse, les chants du fiancé et les chants de la fiancée, le bruit de la meule et la lumière de la lampe.
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 Tout ce pays sera une solitude, un désert, et ces nations seront asservies au roi de Babylone pendant soixante-dix ans.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 Et lorsque les soixante-dix ans seront accomplis, je ferai rendre compte de leur péché au roi de Babylone et à cette nation, — oracle de Yahweh, — et au pays des Chaldéens, et j’en ferai des solitudes éternelles.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 Et je ferai venir sur ce pays toutes les paroles que j’ai prononcées contre lui, tout ce qui est écrit dans ce livre, ce que Jérémie a prophétisé sur toutes les nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 Car des nations nombreuses et de grands rois les asserviront, eux aussi, et je leur rendrai selon leurs actions et selon l’œuvre de leurs mains. »
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 Car ainsi m’a parlé Yahweh, Dieu d’Israël: Prends de ma main cette coupe du vin de ma colère et fais-la boire à toutes les nations vers lesquelles je t’en verrai.
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 Elles en boiront, elles chancelleront, elles seront prises de folie devant l’épée que j’enverrai au milieu d’elles.
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 Je pris la coupe de la main de Yahweh et je la fis boire à toutes les nations vers lesquelles Yahweh m’envoyait:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 à Jérusalem et aux villes de Juda, à ses rois, à ses princes, pour en faire une solitude, une désolation, un objet de moquerie et de malédiction, comme cela se voit aujourd’hui;
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 à Pharaon; roi d’Égypte, à ses serviteurs, à ses princes, à tout son peuple;
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 à tout le peuple mélangé; à tous les rois du pays de Uts; à tous les rois du pays des Philistins, à Ascalon, à Gaza, à Accaron et aux restes d’Azoth;
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 à Edom, à Moab et aux fils d’Ammon;
Edom, Mowab da Ammon;
22 à tous les rois de Tyr, et à tous les rois de Sidon, et aux rois des îles qui sont au delà de la mer;
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 à Dédan, à Théma, à Buz et à tous ceux qui se rasent les tempes;
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 à tous les rois d’Arabie, à tous les rois des peuples mélangés qui habitent le désert;
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 à tous les rois de Zambri, à tous les rois d’Elam, et à tous les rois de Médie;
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 à tous les rois du septentrion, proches ou éloignés, à l’un comme à l’autre, et à tous les royaumes du monde qui sont sur la face de la terre; et le roi de Sésac boira après eux.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 Tu leur diras: Ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d’Israël: Buvez, enivrez-vous, vomissez et tombez pour ne plus vous relever, devant l’épée que j’envoie au milieu de vous.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 Et s’ils refusent de prendre de ta main la coupe pour boire, tu leur diras: Ainsi parle Yahweh: Vous boirez!
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 Car voici: c’est dans la ville sur laquelle mon nom est invoqué que je commence à faire venir le mal; et vous, vous seriez impunis? Vous ne serez pas impunis, car j’appelle l’épée sur tous les habitants de la terre, — oracle de Yahweh des armées.
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 Et toi, tu leur prophétiseras toutes ces choses, et tu leur diras: Yahweh rugit du haut du ciel; de sa demeure sainte il fait retentir sa voix; il rugit violemment contre son domaine; il pousse le cri des vendangeurs, contre tous les habitants de la terre.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 Le bruit en est arrivé jusqu’au bout de la terre; car Yahweh fait le procès à toutes les nations, il entre en jugement avec toute chair; il livre les méchants au glaive, — oracle de Yahweh.
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Ainsi parle Yahweh des armées: Voici que le malheur passe de nation en nation; une grande tempête s’élève des extrémités de la terre.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 Et il y aura des tués de Yahweh, en ce jour-là, d’un bout de la terre à l’autre; ils ne seront ni pleurés, ni ramassés, ni enterrés; ils seront comme du fumier sur le sol.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Hurlez, pasteurs, et criez; roulez-vous dans la poussière, chefs du troupeau, car vos jours sont accomplis pour le massacre; je vous disperserai et vous tomberez comme des vases de prix.
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 Plus de retraite pour les pasteurs, plus de refuge pour les chefs du troupeau!
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 On entend les cris des pasteurs, et les hurlements des chefs du troupeau, car Yahweh ravage leur pâturage.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 Les campagnes paisibles sont dévastées par la fureur de la colère de Yahweh.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 Il quitte sa retraite, comme le lion son fourré; leur pays va être changé en désert devant la fureur du destructeur, devant la colère de Yahweh.
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.

< Jérémie 25 >