< Jérémie 2 >

1 La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Va et crie aux oreilles de Jérusalem en ces termes: Ainsi parle Yahweh: Je me suis souvenu de la piété de ta jeunesse, de l’amour de tes fiançailles, alors que tu me suivais au désert, au pays qu’on n’ensemence pas.
“Tafi ka yi shela a kunnuwar Urushalima cewa, “‘Na tuna da amincin ƙuruciyarki, yadda kamar amarya kika ƙaunace ni kika kuma bi ni cikin hamada, cikin ƙasar da ba a yi shuka ba.
3 Israël était la chose consacré à Yahweh, les prémices de son revenu; quiconque en mangeait se rendait coupable; le malheur fondait sur lui, — oracle de Yahweh.
Isra’ila tsattsarka ce ga Ubangiji, nunan fari na girbinsa; dukan waɗanda suka cinye ta an same su da laifi, masifa kuwa ta same su,’” in ji Ubangiji.
4 Ecoutez la parole de Yahweh, maison de Jacob, et vous toutes, familles de la maison d’Israël:
Ka saurari maganar Ubangiji, ya gidan Yaƙub, dukanku zuriyar gidan Isra’ila.
5 Ainsi parle Yahweh: Quelle iniquité vos pères ont-ils trouvé en moi, pour s’éloigner de moi, pour suivre la vanité et devenir eux-mêmes vanité?
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Wane laifi ne kakanninku sun same ni da shi, da suka tsaya nesa da ni? Sun bi gumakan banza su kansu suka kuma zama banza da kansu.
6 Ils n’ont pas dit: « Où est Yahweh, qui nous a fait monter du pays d’Égypte, qui nous a guidés dans le désert, dans le pays aride et crevassé, dans le pays de sécheresse et d’ombre de mort, dans le pays où nul homme ne passe, et où personne n’habite? »
Ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji, wanda ya fitar da su daga Masar ya bishe su cikin jeji cikin hamada da kwazazzabai ƙasa mai fări da kuma duhu, ƙasar da ba kowa mai ratsa ta ba kowa kuma mai zama a cikinta?’
7 Et je vous ai fait venir dans un pays semblable à un verger, pour en manger les fruits et les biens, et, une fois entrés, vous avez souillé mon pays, et fait de mon héritage une abomination.
Na kawo ku zuwa ƙasa mai albarka don ku ci amfaninta da abubuwa masu yalwar da take bayarwa. Amma kuka zo kuka ƙazantar da ƙasata kuka kuma mai da gādona abin ƙyama.
8 Les prêtres n’ont pas dit: « Où est Yahweh? » Les dépositaires de la loi ne m’ont pas connu; les pasteurs m’ont été infidèles, et les prophètes ont prophétisé par Baal; et ils ont suivi ceux qui ne sont d’aucun secours.
Firistoci ba su yi tambaya, ‘Ina Ubangiji ba.’ Waɗanda suke amfani da doka ba su san ni ba; shugabanni suka yi mini tawaye. Annabawa suka yi annabci ta wurin Ba’al, suna bin gumakan banza.
9 Aussi je veux encore plaider contre vous, — oracle de Yahweh, et je plaiderai contre les enfants de vos enfants.
“Saboda haka ina sāke tuhumarku,” in ji Ubangiji. “Zan kuma tuhumi’ya’ya’ya’yanku.
10 Passez donc aux îles de Céthim et regardez; envoyez à Cédar et observez bien; et voyez s’il y a là rien de semblable.
Ku ƙetare zuwa tsibiran Kittim ku gani, ku aika zuwa Kedar ku duba da kyau; ku ga ko an taɓa yin wani abu haka.
11 Une nation change-t-elle de dieux? — Et encore ce ne sont pas des dieux!... Et mon peuple a changé sa gloire contre ce qui ne sert à rien!
Akwai wata al’ummar da ta canja allolinta? (Duk da haka su ba alloli ba ne sam.) Amma mutanena sun musayar da ɗaukakarsu da gumakan banza.
12 Cieux, étonnez-vous-en, frémissez d’horreur et soyez stupéfaits, oracle de Yahweh!
Ku girgiza saboda wannan, ya sammai, ku kuma razana don tsoro mai girma,” in ji Ubangiji.
13 Car mon peuple a fait double mal: ils m’ont abandonné, moi, la source des eaux vives, pour se creuser des citernes, des citernes crevassées, qui ne retiennent pas l’eau.
“Mutanena sun aikata zunubai guda biyu. Sun rabu da ni, ni da nake maɓulɓular ruwan rai, sun kuma haƙa tankunan ruwansu, tankuna ruwan da suka fashe da ba za su iya riƙe ruwa ba.
14 Israël est-il un esclave, est-il né d’un esclave dans la maison? Pourquoi donc est-il traité comme un butin?
Isra’ila bawa ne, bawa ne ta wurin haihuwa? Me ya sa ya zama ganima?
15 Contre lui les lionceaux rugissent, poussent leurs cris, et ils mettent son pays en dévastation. Ses villes sont incendiées, sans d’habitants.
Zakoki sun yi ruri; sun yi masa ruri. Sun lalatar da ƙasarsa; an ƙone garuruwansa aka kuma watse daga ciki.
16 Même les fils de Noph et de Taphnès te tondent le crâne!
Haka ma, mutanen Memfis da Tafanes sun aske rawanin kanka
17 Cela ne t’arrive-t-il pas parce que tu as abandonné Yahweh, ton Dieu, au temps où il te dirigeait dans la voie?
Ba kai ne ba ka jawo wa kanka ba ta wurin rabuwa da Ubangiji Allahnka sa’ad da ya bi da kai a hanya?
18 Et maintenant qu’as-tu à faire sur la route de l’Égypte, pour aller boire l’eau du Nil, et qu’as-tu à faire sur la route de l’Assyrie, pour aller boire l’eau du fleuve?
To, me ya sa za ka Masar don shan ruwa daga Shihor? Kuma me ya sa za ka Assuriya don shan ruwa daga Kogi?
19 Ton impiété te châtie et tes rébellions te punissent! Sache donc et vois combien il est mauvais et amer d’avoir abandonné Yahweh, ton Dieu, et de n’avoir de moi aucune crainte, — oracle du Seigneur Yahweh des armées.
Muguntarka za tă hukunta ka; jan bayanka zai tsawata maka. Sai ka lura ka kuma gane yaya mugu da kuma ɗaci suke a gare ka sa’ad da ka rabu da Ubangiji Allahnka kuma ba ka tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
20 Car depuis longtemps tu as brisé ton joug, tu as rompu tes liens et tu as dit: « Je ne servirai plus! » Car sur toute colline élevée et sous ton arbre vert tu t’es étendue, comme une courtisane.
“Tun da daɗewa ka karya karkiyarka ka kuma tsintsinke sarƙoƙinka; sai ka ce, ‘Ba zan bauta maka ba!’ Tabbatacce, a kan kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane ɗanyen itace ka kwanta kamar karuwa.
21 Et moi, je t’avais plantée comme une vigne excellente, tout entière d’une souche franche. Comment t’es-tu changée pour moi en sarments bâtards d’une vigne étrangère?
Na shuka ka kamar zaɓaɓɓen inabi iri mai kyau da kuma wanda za a dogara a kai. Yaya kuma ka juya kana gāba da ni ka lalace, ka zama inabin jeji?
22 Oui, quand tu te laverais à la soude, et que tu prodiguerais la potasse, ton iniquité ferait tache devant moi, — oracle du Seigneur Yahweh.
Ko da yake ka wanke kanka da sabulu ka yi amfani da sabulu mai yawa, duk da haka har yanzu tabon laifinka yana nan a gabana,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
23 Comment dis-tu: « Je ne me suis pas souillée; je ne suis pas allée après les Baals? » Vois les traces de tes pas dans la Vallée; reconnais ce que tu as fait! Chamelle légère, croisant ses pas en tout sens,
“Yaya za ka ce, ‘Ban ƙazantu ba; ban bi Ba’al ba’? Duba yadda ka yi a cikin kwari; ka ga abin da ka yi. Kai kamar makwaɗaciyar raƙuma ce mai zafin gudu kana gudu nan da can,
24 onagre habituée au désert, dans l’ardeur de sa passion, elle aspire l’air: qui l’empêchera de satisfaire son désir? Nul de ceux qui la recherchent n’a à se fatiguer; ils la trouvent en son mois.
kamar jakar jejin da ta saba da hamada, mai busar iska cikin son barbaranta sa’ad da take son barbara wa zai iya hana ta? Jakin da yake nemanta, ba ya bukatar wahalar da kansa; a lokacin barbara za a same ta.
25 Prends garde que ton pied ne se trouve à nu, et que ton gosier ne se dessèche! Mais tu dis: « Inutile! Non, car j’aime les étrangers et j’irai après eux! »
Kada ka yi gudu har ƙafafunka su zama ba takalma maƙogwaronka kuma ya bushe. Amma sai ka ce, ‘Ba amfani! Ina ƙaunar baƙin alloli kuma dole in bi su.’
26 Comme un voleur pris sur le fait est couvert de honte, ainsi ont été confondus la maison d’Israël, eux, leurs rois, leurs chefs, leurs prêtres et leurs prophètes,
“Kamar yadda akan kunyatar da ɓarawo sa’ad da aka kama shi, haka gidan Isra’ila zai sha kunya, su, sarakunansu da shugabanninsu, firistocinsu da kuma annabawansu.
27 qui disent au bois: « Tu es mon père, » et à la pierre: « Tu m’as mis au monde. » Car ils m’ont tourné le dos, et non la face, et au temps de leur malheur ils disent: « Lève-toi et sauve-nous! »
Kuna ce wa itace, ‘Kai ne mahaifina,’ ga dutse kuma, ‘Kai ne ka haife ni.’ Sun juye mini bayansu ba fuskokinsu ba; duk da haka sa’ad da suna cikin wahala, sukan ce, ‘Zo ka cece mu!’
28 Où sont donc les dieux que tu t’es faits? Qu’ils se lèvent, s’ils peuvent te sauver au temps de ton malheur! Car aussi nombreux que tes villes sont tes dieux, ô Juda.
To ina allolin da kuka yi wa kanku? Bari su zo in suna iya cetonku sa’ad da kuke cikin wahala! Gama kuna da alloli masu yawa kamar yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda.
29 Pourquoi plaidez-vous contre moi? Vous m’avez tous été infidèles, — oracle de Yahweh.
“Me ya sa kuke tuhumana? Dukanku kun yi mini tawaye,” in ji Ubangiji.
30 C’est en vain que j’ai frappé vos fils; ils n’en ont pas retiré d’instruction; votre épée a dévoré vos prophètes, comme un lion destructeur.
“A banza na hukunta mutanenku; ba su yi gyara ba. Takobinku ya cinye annabawanku kamar zaki mai jin yunwa.
31 Quelle race vous êtes! Considérez la parole de Yahweh: Ai-je été pour Israël un désert, un pays d’épaisses ténèbres? Pourquoi mon peuple a-t-il dit: « Nous sommes libres, nous ne reviendrons pas à vous? »
“Ku na wannan zamani, ku saurari maganar Ubangiji. “Na zama wa Isra’ila hamada ne ko ƙasa mai babban duhu? Me ya sa mutanena suke cewa, ‘Muna da’yanci mu yi ta yawo; ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
32 Une vierge oublie-t-elle sa parure, une fiancée sa ceinture? Et mon peuple m’a oublié depuis des jours sans nombre!
Budurwa za tă manta da kayan adonta amarya ta manta da kayan adon aurenta? Duk da haka mutanena sun manta da ni, kwanaki ba iyaka.
33 Que tu sais bien disposer tes voies pour chercher l’amour! Pour cela, même avec le crime tu familiarises tes voies!
Kuna da azanci sosai a bin masoya! Kai, ko mafiya muni cikin mata tana iya koya daga hanyoyinku.
34 Jusque sur les pans de tes vêtements, on trouve le sang des pauvres innocents; tu ne les avais pas surpris en délit d’effraction, mais tu les as tués pour toutes ces choses.
A rigunanku mutane kan sami jinin matalauta marasa laifi, ko da yake ba ku kama su suna fasawa su shiga ba. Duk da haka
35 Et tu dis: « Oui, je suis innocente; certainement sa colère s’est détournée de moi. » Me voici pour te faire le procès sur ce que tu dis: « Je n’ai pas péché! »
kuna cewa, ‘Ba ni da laifi; ba ya fushi da ni.’ Amma zan zartar da hukunci a kanku domin kun ce, ‘Ban yi zunubi ba.’
36 Quelle hâte tu mets à changer ta voie! Tu seras rendue confuse par l’Égypte, comme tu l’as été par l’Assyrie.
Don me kuke yawo da yawa haka, kuna ta canjin hanyoyinku? Masar za tă kunyata ku yadda kuka sha kunya a wurin Assuriya.
37 De là aussi tu reviendras, les mains sur la tête; car Yahweh a rejeté ceux en qui tu mets ta confiance, et tu ne réussiras pas avec eux.
Za ku kuma bar wurin da hannuwanku a kanku, gama Ubangiji ya ƙi waɗanda kuka amince da su; ba za ku zama abin taimako a gare su ba.

< Jérémie 2 >