< Isaïe 7 >

1 Il arriva du temps d’Achaz, fils de Joatham, fils d’Ozias, roi de Juda, que Rasin, roi de Syrie, avec Phacée, fils de Romélie, roi d’Israël, monta contre Jérusalem pour l’attaquer; mais il ne put s’en emparer.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 On annonça à la maison de David cette nouvelle: « La Syrie est campée en Ephraïm. » Alors le cœur du roi et le cœur de son peuple furent agités comme les arbres de la forêt sont agités par le vent.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Et Yahweh dit à Isaïe: « Sors à la rencontre d’Achaz, toi et Schéar-Jasub, ton fils, vers l’extrémité du canal de l’étang supérieur, sur le chemin du champ du foulon.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 Et tu lui diras: Prends garde, tiens-toi tranquille, ne crains point, et que ton cœur ne défaille pas devant ces deux bouts de tisons fumants, à cause de la fureur de Rasin et de la Syrie, et du fils de Romélie.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Parce que la Syrie a médité le mal contre toi ainsi qu’Ephraïm et le fils de Romélie, en disant:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 « Montons contre Juda, jetons-le dans l’épouvante, envahissons-le, et établissons-y pour roi le fils de Tabéel;
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 ainsi parle le Seigneur Yahweh: Cela n’aura pas d’effet, cela ne sera pas!
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 Car la tête de la Syrie, c’est Damas, et la tête de Damas, c’est Rasin; et encore soixante-cinq ans, et Ephraïm aura cessé d’être un peuple.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Et la tête d’Ephraïm, c’est Samarie, et la tête de Samarie, c’est le fils de Romélie. Si vous ne croyez pas, vous ne subsisterez pas! »
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 Yahweh parla encore à Achaz, en disant:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 « Demande un signe à Yahweh, ton Dieu, demande-le dans les profondeurs du schéol ou dans les hauteurs du ciel. » (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 Mais Achaz dit: « Je ne le demanderai pas, je ne tenterai pas Yahweh. »
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Et Isaïe dit: « Ecoutez, maison de David: Est-ce trop peu pour vous de fatiguer les hommes, que vous fatiguiez aussi mon Dieu?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 C’est pourquoi le Seigneur lui-même vous donnera un signe: Voici que la Vierge a conçu, et elle enfante un fils, et elle lui donne le nom d’Emmanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 Il mangera de la crème et du miel, jusqu’à ce qu’il sache rejeter le mal et choisir le bien.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 Car avant que l’enfant sache rejeter le mal et choisir le bien, le pays dont tu redoutes les deux rois sera dévasté.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Yahweh fera venir sur toi et sur ton peuple, et sur la maison de ton père, des jours tels qu’il n’en est pas venu depuis le jour où Ephraïm s’est séparé de Juda, — le roi d’Assyrie. »
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 En ce jour-là, Yahweh sifflera la mouche qui est à l’extrémité des fleuves d’Égypte, et l’abeille qui est au pays d’Assyrie.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 Elles viendront et se poseront toutes dans les vallées escarpées et dans les fentes des rochers, sur tous les buissons et sur tous les pâturages.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 En ce jour-là, le Seigneur rasera avec un rasoir qu’il aura loué au delà du Fleuve — avec le roi d’Assyrie, — la tête et le poil des pieds, et il enlèvera aussi la barbe.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 En ce jour-là, un homme nourrira une vache et deux brebis,
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 et, à cause de l’abondance du lait qu’elles donneront, on ne mangera plus que de la crème; car c’est de la crème et du miel que mangeront tous ceux qui seront restés dans le pays.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 En ce jour-là, tout endroit où il y avait mille ceps de vigne, valant mille pièces d’argent, sera couvert de ronces et d’épines.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 On y entrera avec des flèches et avec l’arc, car tout le pays ne sera que ronces et épines.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 Et sur toutes les montagnes que l’on cultivait avec le sarcloir, tu n’iras plus, par crainte des ronces et des épines, elles seront un pâturage de bœufs, et une terre foulée par les brebis.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaïe 7 >