< Isaïe 4 >
1 Sept femmes saisiront un seul homme en ce jour, et diront: « Nous mangerons notre pain, et nous nous vêtirons de nos habits; permets seulement que nous portions ton nom; ôte notre opprobre. »
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 En ce jour-là, le germe de Yahweh fera l’ornement et la gloire, et le fruit de la terre, fera l’orgueil et la parure des réchappés d’Israël.
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 Et ceux qui seront restés dans Sion, et ceux qui auront été épargnés dans Jérusalem seront appelés saints, tous ceux qui sont inscrits pour la vie dans Jérusalem.
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 Quand Yahweh aura lavé les souillures des filles de Sion, et purifié Jérusalem du sang qui est au milieu d’elle, par l’esprit de jugement et par l’esprit d’extermination,
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 alors Yahweh créera sur toute l’étendue de la montagne de Sion, et sur ses assemblées, une nuée durant le jour et une fumée, et l’éclat d’une flamme ardente pendant la nuit. Car sur toute sa gloire il y aura un dais;
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 et il y aura une tente pour donner de l’ombrage contre les ardeurs du jour, et pour servir de refuge et d’abri contre l’orage et la pluie.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.