< Isaïe 38 >
1 En ce temps-là, Ezéchias fut malade à la mort. Le prophète Isaïe, fils d’Amos, vint auprès de lui et lui dit: « Ainsi dit Yahweh: Donne tes ordres à ta maison, car tu vas mourir, et tu ne vivras plus. »
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2 Ezéchias tourna son visage contre le mur et pria Yahweh; il dit:
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3 « Souvenez-vous, ô Yahweh, que j’ai marché devant votre face avec fidélité et intégrité, et que j’ai fait ce qui est bien à vos yeux! » Et Ezéchias versa des larmes abondantes.
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 Et la parole de Yahweh fut adressée à Isaïe en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Ishaya cewa,
5 « Va, et dis à Ezéchias: « Ainsi dit Yahweh, le Dieu de David, ton père: J’ai entendu ta prière, j’ai vu tes larmes; voici que j’ajouterai à tes jours quinze années.
“Ka tafi ka faɗa wa Hezekiya, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, ya ce na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan ƙara maka shekaru goma sha biyar ga rayuwarka.
6 Je te délivrerai, toi et cette ville, de la main du roi d’Assyrie; je protégerai cette ville.
Zan kuwa cece ka da wannan birni daga hannun sarkin Assuriya. Zan kiyaye wannan birni.
7 Et voici pour toi le signe donné par Yahweh, auquel tu connaîtras que Yahweh accomplira cette parole qu’il a dite:
“‘Ga alamar Ubangiji gare ka cewa Ubangiji zai aikata kamar yadda ya yi alkawari.
8 Voici que je vais faire reculer l’ombre en arrière, des degrés qu’elle a descendus sur les degrés d’Achaz sous l’influence du soleil, soit de dix degrés. Et le soleil recula de dix degrés sur les degrés qu’il avait descendus.
Zan sa inuwar da rana ta yi a kan matakalar Ahaz ta koma baya da taki goma.’” Saboda haka inuwar ta koma da baya daga fuskar rana har taki goma.
9 Ecrit d’Ezéchias, roi de Juda, lorsqu’il fut malade et qu’il guérit de sa maladie:
Rubutun Hezekiya sarkin Yahuda bayan ciwonsa da kuma warkarwarsa.
10 Je disais: Dans la paix de mes jours je m’en vais aux portes du schéol; je suis privé du reste de mes ans! (Sheol )
Na ce, “Cikin tsakiyar rayuwata dole in bi ta ƙofofin mutuwa a kuma raba ni da sauran shekaruna?” (Sheol )
11 Je disais: Je ne verrai plus Yahweh, Yahweh sur la terre des vivants; je ne verrai plus les hommes, parmi les habitants du silencieux séjour!
Na ce, “Ba zan ƙara ganin Ubangiji ba, Ubangiji a ƙasa ta masu rai; ba zan ƙara ga wani mutum, ko in kasance tare da waɗanda suke zama a wannan duniya ba.
12 Ma demeure est enlevée, emportée loin de moi comme une tente de bergers. Comme un tisserand, j’ourdissais ma vie; il me retranche du métier! Du jour à la nuit tu en auras fini avec moi!
Kamar tentin makiyayi an rushe gidana aka kuma ƙwace ta daga gare ni. Kamar mai saƙa, na nannaɗe rayuwata, ya kuma yanke ni daga sandar saƙa; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
13 Je me suis tu jusqu’au matin; comme un lion, il brisait tous mes os; du jour à la nuit tu en auras fini avec moi!
Na yi jira da haƙuri har safiya, amma kamar zaki ya kakkarya ƙasusuwana duka; dare da rana ka kawo ni ga ƙarshe.
14 Comme l’hirondelle, comme la grue, je crie; je gémis comme la colombe; mes yeux se sont lassés à regarder en haut: « Yahweh, on me fait violence; sois mon garant! »
Na yi kuka kamar mashirare ko zalɓe, na yi kuka kamar kurciya mai makoki. Idanuna suka rasa ƙarfi yayinda na duba sammai. Na damu; Ya Ubangiji, ka taimake ni!”
15 Que dirais-je? Il m’a dit, il l’a fait. Je marcherai humblement pendant toutes mes années, me souvenant de l’amertume de mon âme.
Amma me zan ce? Ya riga ya yi mini magana, shi kansa ne kuma ya aikata. Zan yi tafiya da tawali’u dukan kwanakina saboda wahalar raina.
16 Seigneur, c’est en cela qu’est la vie, en tout cela est la vie de mon esprit. Vous me guérissez, vous me rendez la vie:
Ubangiji, ta waɗannan abubuwa ne mutane suke rayuwa; ruhuna kuma yana samun rai a cikinsu shi ma. Ka maido mini da lafiya ka kuma sa na rayu.
17 voici que ma suprême amertume se change en paix! Vous avez retiré mon âme de la fosse de perdition; vous avez jeté derrière votre dos tous mes péchés.
Tabbatacce wannan kuwa saboda ribata ne cewa in sha irin wahalan nan. Cikin ƙaunarka ka kiyaye ni daga ramin hallaka; ka sa dukan zunubaina a bayanka.
18 Car le schéol ne vous célèbre pas, la mort ne chante pas vos louanges; ceux qui descendent dans la fosse n’espèrent plus en votre fidélité. (Sheol )
Gama kabari ba zai yabe ka ba, matattu ba za su rera yabonka ba; waɗanda suka gangara zuwa rami ba za su sa zuciya ga amincinka ba. (Sheol )
19 Le vivant, le vivant, c’est lui qui vous célèbre, comme je le fais en ce jour; père fera connaître à ses enfants votre fidélité.
Masu rai, masu rai, su suke yabonka, kamar yadda nake yi a yau; iyaye za su faɗa wa’ya’yansu game da amincinka.
20 Yahweh a été prompt à me sauver; nous ferons résonner les cordes de ma harpe; tous les jours de notre vie, devant la maison de Yahweh.
Ubangiji zai cece ni, za mu kuma rera da kayan kiɗi masu tsirkiya dukan kwanakinmu a cikin haikalin Ubangiji.
21 Isaïe dit: « Qu’on apporte une masse de figues, et qu’on l’applique sur l’ulcère et que le roi guérisse! »
Ishaya ya riga ya ce, “Ku shirya curin da aka yi da’ya’yan ɓaure ku kuma shafa a marurun, zai kuwa warke.”
22 Et Ezéchias dit: « A quel signe connaîtrai-je que je monterai à la maison de Yahweh? »
Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan haura zuwa haikalin Ubangiji?”