< Isaïe 31 >

1 Malheur à ceux qui descendent en Égypte chercher du secours, qui s’appuient sur les chevaux, mettent leur confiance dans les chars, parce qu’ils sont nombreux, et dans les cavaliers, parce qu’ils sont forts, mais ne regardent pas vers le Saint d’Israël, et ne recherchent pas Yahweh.
Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
2 Cependant il est sage, il fait venir le malheur, il ne révoque pas ses paroles; il s’élèvera contre la maison des méchants, et contre le secours de ceux qui commettent l’iniquité.
Shi ma yana da hikima kuma zai iya kawo masifa; ba ya janye kalmominsa. Zai yi gāba da gidan mugu, gāba da waɗanda suke taimakon masu aikata mugunta.
3 L’Egyptien est un homme, et non un Dieu; ses chevaux sont chair, et non esprit; Yahweh étendra sa main, celui qui secourt trébuchera, et le secouru tombera, et ils périront tous ensemble.
Amma Masarawa mutane ne ba Allah ba; dawakansu nama da jini ne ba ruhu ba. Sa’ad da Ubangiji ya miƙa hannunsa, shi da yake taimako zai yi tuntuɓe shi da aka taimaka zai fāɗi; dukansu biyu za su hallaka tare.
4 Car ainsi m’a parlé Yahweh: comme le lion rugit, ainsi que le jeune lion, sur sa proie, alors que se rassemble contre lui la multitude des bergers, sans se laisser effrayer par leurs cris, ni troubler par leur nombre: ainsi Yahweh des armées descendra pour combattre, sur la montagne de Sion et sur sa colline.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Kamar yadda zaki kan yi ruri babban zaki a kan abin da ya yi farauta, kuma ko da yake dukan ƙungiyar makiyaya sun taru wuri ɗaya a kansa, ba zai jijjigu ta wurin ihunsu ba ko ya damu da kiraye-kirayensu, ta haka Ubangiji Maɗaukaki zai sauko don yă yi yaƙi a kan Dutsen Sihiyona da kuma a kan ƙwanƙolinsa.
5 Comme des oiseaux déployant leurs ailes sur leur couvée, ainsi Yahweh des armées couvrira Jérusalem; il couvrira, il sauvera, il passera, il délivrera.
Kamar tsuntsaye masu shawagi a sama haka Ubangiji Maɗaukaki zai kiyaye Urushalima; zai kāre ta ya kuma fanshe ta, zai ‘ƙetare’ ta ya kuma kuɓutar da ita.”
6 Revenez donc à celui dont vous vous êtes tant éloignés, enfants d’Israël.
Ku dawo gare shi ku da kuka yi masa babban tayarwa, ya Isra’ilawa.
7 Car en ce jour-là chacun rejettera ses idoles d’argent et ses idoles d’or, que vous avez fabriquées de vos mains pour pécher.
Gama a wannan rana kowannenku zai ƙi gumakan azurfa da zinariya da hannuwanku masu zunubi suka yi.
8 Et Assur tombera par une épée qui n’est pas de l’homme; une épée qui n’est pas d’un mortel le dévorera; il fuiera devant l’épée, et ses jeunes gens seront assujettis au tribut.
“Za a karkashe Assuriyawa da takobin da ba na yin mutum ba; takobi, da ba na yin mutum ba, zai cinye. Za su gudu daga takobi za a kuma sa samarinsu aikin dole.
9 Son rocher fuira d’épouvante, et ses princes tremblants déserteront l’étendard. — oracle de Yahweh, qui a son feu dans Sion, et sa fournaise dans Jérusalem.
Kagararsu za tă fāɗi saboda razana; da ganin matsayin yaƙin, shugabannin yaƙinsu za su firgita,” in ji Ubangiji, wanda wutarsa tana a Sihiyona, wanda matoyarsa tana a Urushalima.

< Isaïe 31 >