< Isaïe 23 >
1 Oracle sur Tyr. Hurlez, navires de Tarsis, car elle est détruite! Plus de maisons, plus d’entrée! C’est du pays de Céthim qu’ils en reçoivent la nouvelle.
Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
2 Soyez dans la stupeur, habitants de la côte, que remplissaient les marchands de Sidon, parcourant la mer.
Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
3 A travers les grandes eaux, le blé du Nil, les moissons du fleuve étaient son revenu; elle était le marché des nations!
A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
4 Rougis de honte, Sidon, car la mer a parlé, la citadelle de la mer, en disant: « Je n’ai pas été en travail, je n’ai pas enfanté, je n’ai pas nourri de jeunes gens, et je n’ai pas élevé de vierges.
Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
5 Quand l’Égypte en apprendra la nouvelle, elle sera saisie d’effroi à la nouvelle de la chute de Tyr.
Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
6 Passez à Tarsis et hurlez, habitants de la côte!
Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
7 Est-ce là votre cité joyeuse, dont l’origine remontait aux jours anciens, et que ses pieds portaient au loin pour y séjourner?
Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
8 Qui a décidé cela contre Tyr, qui donnait des couronnes, dont les marchands étaient des princes, et les trafiquants des grands de la terre?
Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
9 C’est Yahweh des armées qui l’a décidé, pour flétrir l’orgueil de tout ce qui brille, pour humilier tous les grands de la terre.
Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10 Répands-toi dans ton pays, comme le Nil, fille de Tarsis, car tu n’as plus de ceinture.
Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
11 Yahweh a étendu sa main sur la mer, il a fait trembler les royaumes; il a décrété contre Canaan la ruine de ses forteresses.
Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
12 Et il a dit: « Tu ne te livreras plus à la joie, vierge déshonorée, fille de Sidon! Lève-toi, passe à Céthim; là même, plus de repos pour toi.
Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
13 Vois le pays des Chaldéens, de ce peuple qui n’était pas, et qui a livré Assur aux bêtes du désert; ils ont élevé leurs tours, détruit ses palais, ils en ont fait un monceau de ruines. »
Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
14 Hurlez, navires de Tarsis, car votre forteresse est détruite.
Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
15 Il arrivera, en ce jour-là, que Tyr sera oubliée soixante-dix ans, la durée des jours d’un roi. Et au bout de soixante dix ans, il en sera de Tyr comme dans la chanson de la courtisane:
A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16 « Prends ta harpe, fais le tour de la ville, courtisane oubliée; joue avec art, multiplie tes chants, pour qu’on se souvienne de toi. »
“Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
17 Et il arrivera, au bout de soixante-dix ans, que Yahweh visitera Tyr, et elle recevra de nouveau son salaire, et elle se prostituera à tous les royaumes de la terre, sur la face du monde.
A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18 Et son gain et son salaire seront consacrés à Yahweh; ils ne seront ni amassés, ni mis en réserve; car son gain appartiendra à ceux qui habitent devant Yahweh; pour qu’ils mangent, se rassasient et se parent magnifiquement.
Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.