< Osée 12 >

1 Ephraïm se repaît de vent, et il court après le vent d’orient. Tout le jour il accumule le mensonge et la violence; ils concluent alliance avec Assur, et l’huile est transportée en Égypte.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 Yahweh a aussi procès avec Juda; il va châtier Jacob selon ses voies, il lui rendra selon ses œuvres.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 Dans le sein de sa mère, Jacob supplanta son frère, et dans sa vigueur il lutta avec Dieu.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 Il lutta avec l’ange et il eut le dessus; il pleura et lui demanda grâce; il le trouva ensuite à Béthel, et là Dieu a parlé avec nous.
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 Or Yahweh est le Dieu des armées, son nom est Yahweh.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Et toi, tu reviendras à ton Dieu; garde la bonté et la justice, et espère en ton Dieu toujours.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 Canaan tient dans sa main une balance fausse, il aime à extorquer.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 Ephraïm dit: « Pourtant je me suis enrichi, je me suis fait une fortune; dans tous mes gains, on ne trouvera pas pour moi un tort qui soit un péché. »
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 Et moi je suis Yahweh, ton Dieu, depuis le pays d’Égypte; je te ferai encore habiter dans les tentes, comme aux jours de fête.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 Et j’ai parlé aux prophètes, et moi, j’ai multiplié la vision; et, par l’intermédiaire des prophètes, j’ai parlé en paraboles.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 Si Galaad est vanité, ils ne seront que néant; à Galgal, ils ont sacrifié des taureaux; aussi leurs autels seront comme des monceaux de pierres, sur les sillons des champs.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Jacob s’enfuit dans la plaine d’Aram; Israël servit pour une femme, et pour une femme il garda les troupeaux.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 Et par un prophète, Yahweh fit monter Israël hors d’Égypte, et par un prophète il fut gardé.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Ephraïm a provoqué amèrement la colère divine; Il laissera tomber son sang sur lui, et son Seigneur lui rendra son outrage.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.

< Osée 12 >