< Aggée 1 >

1 La deuxième année du roi Darius, au sixième mois, le premier jour du mois, la parole de Yahweh fut adressée, par l’intermédiaire d’Aggée, le prophète, à Zorobabel, fils de Salathiel, gouverneur de Juda, et à Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, en ces termes:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Ainsi parle Yahweh des armées: Ce peuple dit: « Le temps n’est pas venu, le temps pour la maison de Yahweh d’être rebâtie. »
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 Et la parole de Yahweh se fit entendre par l’intermédiaire d’Aggée, le prophète, en ces termes:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 Est-il temps pour vous autres d’habiter vos maisons lambrissées, quand cette maison-là est en ruines?
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Et maintenant ainsi parle Yahweh des armées: Considérez attentivement vos voies.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Vous avez semé beaucoup et recueilli peu; vous mangez, mais non jusqu’à être rassasiés; vous buvez, mais non jusqu’à votre soûl; vous êtes vêtus, mais non jusqu’à être réchauffés; et le salarié gagne son salaire pour une bourse trouée.
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Ainsi parle Yahweh des armées: Considérez attentivement vos voies.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Allez à la montagne, apportez du bois, et bâtissez la maison; j’en aurai plaisir et gloire, dit Yahweh.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 Vous comptiez sur beaucoup, et voici que cela se réduit à peu; vous aviez rentré vos récoltes, et j’ai soufflé dessus. A cause de quoi — oracle de Yahweh des armées? A cause de ma maison qui est en ruines, tandis que vous vous empressez chacun pour votre maison.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 C’est pourquoi les cieux vous ont retenu la rosée, et la terre a retenu ses fruits.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 J’ai appelé la sécheresse sur la terre et sur les montagnes, sur le blé, sur le vin nouveau, sur l’huile, et sur ce que peut produire le sol, et sur l’homme et sur les bêtes; et sur tout le travail des mains.
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Alors Zorobabel, fils de Salathiel, et Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et tout le reste du peuple, écoutèrent la voix de Yahweh, leur Dieu, et les paroles d’Aggée, le prophète, selon la mission qu’il avait reçue de Yahweh, leur Dieu; et le peuple craignit devant Yahweh.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Et Aggée, envoyé de Yahweh, sur l’ordre de Yahweh, parla au peuple en ces termes: « Je suis avec vous, — oracle de Yahweh. »
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 Et Yahweh réveilla l’esprit de Zorobabel, fils de Salathiel, gouverneur de Juda, l’esprit de Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et l’esprit de tout le reste du peuple; et ils vinrent et travaillèrent à la maison de Yahweh des armées, leur Dieu,
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 le vingt-quatrième jour du sixième mois, la deuxième année du roi Darius.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Aggée 1 >