< Genèse 49 >

1 Jacob appela ses fils et leur dit: « Rassemblez-vous, et je vous annoncerai ce qui vous arrivera à la fin des jours.
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 Rassemblez-vous et écoutez, fils de Jacob; écoutez Israël, votre père.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 RUBEN, toi, mon premier-né, ma force, et le premier fruit de ma vigueur, supérieur en dignité et supérieur en puissance,
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 tu as bouillonné comme l’eau; tu n’auras pas la prééminence! Car tu es monté sur la couche de ton père, et tu as souillé ma couche en y montant!
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 SIMÉON et LÉVI sont frères; leurs glaives sont des instruments de violence.
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 Que mon âme n’entre pas dans leur conseil! Que mon âme ne s’unisse pas à leur assemblée! Car, dans leur colère, ils ont égorgé des hommes, et, dans leur emportement, ils ont coupé les jarrets des taureaux.
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 Maudite soit leur colère, car elle a été violente, et leur fureur, car elle a été cruelle! Je les diviserai en Jacob, et je les disperserai en Israël.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Toi, JUDA, tes frères te loueront; ta main sera sur le cou de tes ennemis; les fils de ton père se prosterneront devant toi.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 Juda est un jeune lion. Tu es remonté du carnage, mon fils! Il a ployé les genoux, il s’est couché comme un lion, comme une lionne: qui le fera lever?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 Le sceptre ne s’éloignera pas de Juda, ni le bâton de commandement d’entre ses pieds, jusqu’à ce que vienne Schiloh; c’est à lui que les peuples obéiront.
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 Il attache à la vigne son ânon, au cep le petit de son ânesse; il lave son vêtement dans le vin, son manteau dans le sang de la grappe.
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 Il a les yeux rouges de vin, et les dents blanches de lait.
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 ZABULON habite le bord de la mer, il est sur le rivage où abordent les navires; son flanc est du côté de Sidon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 ISSACHAR est un âne robuste, qui se couche dans ses parcs.
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 Il voit que le repos est bon, et que le pays est agréable; et il courbe son épaule sous le fardeau; il est devenu un homme asservi au tribut.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 DAN juge son peuple, comme l’une des tribus d’Israël.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan est un serpent sur le chemin, une vipère sur le sentier, qui mord les talons du cheval, pour que le cavalier tombe à la renverse.
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 J’espère en ton secours, ô Yahweh!
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 GAD, des bandes armées le pressent, et lui, à son tour, les presse sur les talons.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 D’ASER vient le pain savoureux, il fournit les mets délicats des rois.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 NEPHTALI est une biche en liberté, il prononce des paroles gracieuses.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 JOSEPH est le rejeton d’un arbre fertile, le rejeton d’un arbre fertile sur les bords d’une source; ses branches s’élancent au-dessus de la muraille.
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 Des archers le provoquent, ils lui lancent des flèches et l’attaquent.
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 Mais son arc reste ferme, ses bras et ses mains sont rendus agiles, par les mains du Puissant de Jacob, par celui qui est le Pasteur et le Rocher d’Israël.
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 Que du Dieu de ton père — il t’aidera! — et du Tout-Puissant — il te bénira! te viennent les bénédictions du ciel en haut, les bénédictions de l’abîme en bas, les bénédictions des mamelles et du sein maternel!
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 Les bénédictions de ton père surpassent les bénédictions des montagnes antiques, la beauté des collines éternelles: qu’elles soient sur la tête de Joseph, sur le front du prince de ses frères!
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 BENJAMIN est un loup qui déchire; le matin il dévore la proie, le soir il partage le butin.
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 Ce sont là tous ceux qui formèrent les douze tribus d’Israël; c’est ainsi que leur parla leur père et qu’il les bénit. Il les bénit chacun selon sa bénédiction.
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 Puis il leur donna cet ordre: « Je vais être réuni à mon peuple; enterrez-moi avec mes pères dans la caverne qui est dans le champ d’Ephron, le Hittite,
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 dans la caverne du champ de Macpéla, en face de Mambré, au pays de Canaan: c’est la caverne qu’Abraham a acquise d’Ephron, le Hittite, avec le champ, pour avoir un sépulcre qui lui appartienne.
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 C’est là qu’on a enterré Abraham et Sara, sa femme, c’est là qu’on a enterré Isaac et Rebecca, sa femme, et c’est là que j’ai enterré Lia. »
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
32 Le champ et la caverne qui s’y trouve ont été acquis des fils de Heth.
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 Lorsque Jacob eut achevé de donner ses ordres à ses fils, ayant retiré ses pieds dans le lit, il expira et fut réuni à ses pères.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.

< Genèse 49 >