< Genèse 40 >

1 Après ces choses, il arriva que l’échanson et le panetier du roi d’Égypte offensèrent leur maître, le roi d’Égypte.
Bayan ɗan lokaci, sai mai riƙon kwaf da mai tuyan sarkin Masar suka yi wa maigidansu, sarkin Masar laifi.
2 Pharaon fut irrité contre ses deux officiers, contre le chef des échansons et le chef des panetiers;
Fir’auna ya yi fushi da hafsoshin nan nasa guda biyu, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya,
3 et il les fit enfermer chez le chef des gardes, dans la prison, dans le lieu où Joseph était enfermé.
ya kuma sa su a kurkuku a cikin gidan shugaban masu tsaro, a wannan kurkukun da aka sa Yusuf.
4 Le chef des gardes établit Joseph auprès d’eux, et il les servait; et ils furent un certain temps en prison.
Sai shugaban masu tsaro ya danƙa su a hannun Yusuf, ya kuwa yi musu hidima. Bayan sun jima cikin kurkuku,
5 L’échanson et le panetier du roi d’Égypte, qui étaient enfermés dans la prison, eurent tous deux un songe dans la même nuit, chacun le sien, ayant une signification différente.
sai kowanne a cikin mutum biyun nan, mai riƙon kwaf da mai tuya na sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, suka yi mafarki a dare ɗaya, kuma kowane mafarki ya kasance da fassara irin tasa.
6 Joseph, étant venu le matin vers eux, les regarda; et voici, ils étaient tristes.
Sa’ad da Yusuf ya zo wurinsu kashegari, sai ya ga duk sun damu.
7 Il interrogea donc les officiers de Pharaon qui étaient avec lui en prison, dans la maison de son maître, et leur dit: « Pourquoi avez-vous le visage triste aujourd’hui? »
Saboda haka ya tambayi hafsoshin Fir’auna, waɗanda suke a kurkuku tare da shi, a gidan maigidansa ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a ɓace haka?”
8 Ils lui dirent: « Nous avons eu un songe, et il n’y a personne ici pour l’expliquer. » Et Joseph leur dit: « N’est-ce pas à Dieu qu’appartiennent les interprétations? Racontez-moi, je vous prie, votre songe. »
Sai suka amsa, “Mu biyu, mun yi mafarki, amma babu wani da zai fassara mana su.” Sa’an nan Yusuf ya ce musu, “Fassara ba daga Allah take zuwa ba? Ku faɗa mini mafarkanku.”
9 Le chef des échansons raconta son songe à Joseph, en disant: « Dans mon songe, voici, il y avait un cep devant moi,
Sai shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusuf mafarkinsa. Ya ce masa, “A cikin mafarkina, na ga kuringa a gabana,
10 et ce cep avait trois branches; il poussa des bourgeons, la fleur sortit et ses grappes donnèrent des raisins mûrs.
kuma a kuringar, akwai rassa uku. Nan da nan kuringar ta yi toho, ta huda, ta kuma yi nonna har suka nuna, suka zama inabi.
11 La coupe de Pharaon était dans ma main; je pris des raisins, j’en pressai le jus dans la coupe de Pharaon et je mis la coupe dans la main de Pharaon. »
Kwaf Fir’auna kuwa yana a hannuna, na kuma ɗiba inabin na matse su cikin kwaf Fir’auna, na kuma sa kwaf ɗin a hannunsa.”
12 Joseph lui dit: « En voici l’interprétation: les trois branches sont trois jours.
Yusuf ya ce masa, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Rassan nan uku, kwana uku ne.
13 Encore trois jours, et Pharaon relèvera ta tête et te rétablira dans ta charge, et tu mettras la coupe de Pharaon dans sa main, selon ton premier office, lorsque tu étais son échanson.
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fitar da kai, yă maido da kai a matsayinka, za ka kuwa sa kwaf Fir’auna cikin hannunsa, kamar yadda ka saba yi sa’ad da kake mai riƙon kwaf nasa.
14 Si tu te souviens de moi quand le bonheur te sera rendu, et si tu daignes user de bonté à mon égard, rappelle-moi au souvenir de Pharaon, et fais-moi sortir de cette maison.
Amma fa, sa’ad da kome ya zama maka da kyau, ka tuna da ni, ka kuma yi mini alheri, ka ambace ni wa Fir’auna, ka fid da ni daga wannan kurkuku.
15 Car c’est par un rapt que j’ai été enlevé du pays des Hébreux, et ici même je n’ai rien fait pour qu’on m’ait mis dans cette prison. »
Gama da ƙarfi ne aka ɗauke ni daga ƙasar Ibraniyawa, ko a nan ma ban yi wani abin da ya cancanci a sa ni cikin kurkuku ba.’”
16 Le chef des panetiers, voyant que Joseph avait donné une interprétation favorable, lui dit: « Moi aussi, dans mon songe, voici que j’avais sur la tête trois corbeilles de pain blanc.
Sa’ad da shugaban masu tuya ya ga cewa Yusuf ya ba da fassara mai gamsarwa, sai ya ce, wa Yusuf, “Ni ma na yi mafarki. A kaina, akwai kwanduna uku na burodi.
17 Dans la corbeille de dessus se trouvaient toutes sortes de pâtisseries pour Pharaon, et les oiseaux les mangeaient dans la corbeille qui était sur ma tête. »
A kwandon na bisa, akwai kayan iri-iri da aka toya, masu kyau domin Fir’auna, amma tsuntsaye suka ci su a kwandon da yake kaina.”
18 Joseph répondit: « En voici l’interprétation: les trois corbeilles sont trois jours.
Yusuf ya ce, “Ga abin da mafarkin yake nufi, ‘Kwanduna uku, kwanaki uku ne.
19 Encore trois jours, et Pharaon enlèvera ta tête de dessus toi et te pendra à un bois, et les oiseaux dévoreront ta chair de dessus toi. »
Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’”
20 Le troisième jour, qui était le jour de la naissance de Pharaon, il donna un festin à tous ses serviteurs; et il éleva la tête du chef des échansons et la tête du chef des panetiers:
To, a rana ta uku ne, ranar tunawa da haihuwar Fir’auna, ya kuwa yi biki wa dukan hafsoshinsa. Ya fid da shugaban masu shayarwa da kuma shugaban masu tuya a gaban hafsoshinsa.
21 il rétablit le chef des échansons dans son office d’échanson, et celui-ci mit la coupe dans la main de Pharaon;
Ya mai da shugaban masu shayarwa a matsayinsa, saboda haka shugaban masu shayarwa ya sāke sa kwaf a hannun Fir’auna,
22 et il fit pendre le chef des panetiers, selon l’interprétation que Joseph leur avait donnée.
amma ya rataye shugaban masu tuya, kamar dai yadda Yusuf ya faɗa musu a fassarar mafarkan da suka yi.
23 Mais le chef des échansons ne parla pas de Joseph, et l’oublia.
Shugaban masu shayarwa fa, bai tuna da Yusuf ba; ya mance da shi.

< Genèse 40 >