< Genèse 28 >
1 Isaac appela Jacob et le bénit, et il lui donna cet ordre: « Tu ne prendras pas pour femme une des filles de Canaan.
Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
2 Lève-toi, va en Paddan-Aram, chez Bathuel, père de ta mère, et prends-y une femme parmi les filles de Laban, frère de ta mère.
Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
3 Que Dieu le tout-puissant te bénisse, qu’il te fasse croître et multiplier, afin que tu deviennes une multitude de peuples!
Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
4 Qu’il te donne la bénédiction d’Abraham, à toi et à ta postérité avec toi, afin que tu possèdes le pays où tu séjournes, et que Dieu a donné à Abraham! »
Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
5 Et Isaac congédia Jacob, qui s’en alla en Paddan-Aram, vers Laban, fils de Bathuel l’Araméen, frère de Rebecca, la mère de Jacob et d’Esaü.
Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
6 Esaü vit qu’Isaac avait béni Jacob et qu’il l’avait envoyé en Paddan-Aram pour y prendre une femme, et qu’en le bénissant, il lui avait donné cet ordre: « Tu ne prendras pas pour femme une des filles de Canaan »,
Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
7 et que Jacob, obéissant à son père et à sa mère, était parti pour Paddan-Aram.
ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
8 Esaü vit donc que les filles de Canaan déplaisaient à Isaac, son père,
Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
9 et Esaü s’en alla vers Ismaël, et il prit pour femme, outre les femmes qu’il avait déjà, Mahéleth, fille d’Ismaël, fils d’Abraham, et sœur de Nabaïoth.
saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
10 Jacob partit de Bersabée et s’en alla à Haran.
Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
11 Il arriva dans un lieu; et il y passa la nuit, parce que le soleil était couché. Ayant pris une des pierres qui étaient là, il en fit son chevet, et il se coucha dans ce lieu.
Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
12 Il eut un songe: et voici, une échelle était posée sur la terre et son sommet touchait au ciel; et voici, sur elle des anges de Dieu montaient et descendaient,
Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
13 et au haut se tenait Yahweh. Il dit: « Je suis Yahweh, le Dieu d’Abraham, ton père, et le Dieu d’Isaac. Cette terre sur laquelle tu es couché, je te la donnerai, à toi et à ta postérité.
A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
14 Ta postérité sera comme la poussière de la terre; tu t’étendras à l’occident et à l’orient, au septentrion et au midi, et toutes les familles de la terre seront bénies en toi et en ta postérité.
Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
15 Voici, je suis avec toi, et je te garderai partout où tu iras et je te ramènerai dans ce pays. Car je ne t’abandonnerai pas que je n’aie fait ce que je t’ai dit. »
Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
16 Jacob s’éveilla de son sommeil et il dit: « Certainement Yahweh est en ce lieu, et moi je ne le savais pas! »
Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
17 Saisi de crainte, il ajouta: « Que ce lieu est redoutable! C’est bien ici la maison de Dieu, c’est ici la porte du ciel. »
Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
18 S’étant levé de bon matin, Jacob prit la pierre dont il avait fait son chevet, la dressa pour monument et versa de l’huile sur son sommet.
Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
19 Il nomma ce lieu Béthel; mais primitivement la ville s’appelait Luz.
Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
20 Et Jacob fit un vœu en disant: « Si Dieu est avec moi et me garde dans ce voyage que je fais; s’il me donne du pain à manger et des habits pour me vêtir,
Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
21 et si je retourne heureusement à la maison de mon père, Yahweh sera mon Dieu;
har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
22 cette pierre que j’ai dressée pour monument sera une maison de Dieu, et je vous paierai la dîme de tout ce que vous me donnerez. »
kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”