< Genèse 10 >

1 Voici la postérité des fils de Noé, Sem, Cham et Japheth. Il leur naquit des fils après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Fils de Japheth: Gomer, Magog, Madaï, Javan, Thubal, Mosoch et Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Fils de Gomer: Ascénez, Riphath et Thogorma. —
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Fils de Javan: Elisa et Tharsis, Cetthim et Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 C’est d’eux que viennent les peuples dispersés dans les îles des nations, dans leurs divers pays, chacun selon sa langue, selon leurs familles, selon leurs nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Fils de Cham: Chus, Mesraïm, Phuth et Canaan. —
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Fils de Chus: Saba, Hévila, Sabatha, Regma et Sabathaca. Fils de Regma: Saba et Dadan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Chus engendra Nemrod: celui-ci fut le premier un homme puissant sur la terre.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 Ce fut un vaillant chasseur devant Yahweh; c’est pourquoi l’on dit: « Comme Nemrod, vaillant chasseur devant Yahweh. »
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Le commencement de son empire fut Babel, Arach, Achad et Chalanné au pays de Sennaar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De ce pays il alla en Assur, et bâtit Ninive, Rechoboth-Ir, Chalé,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 et Résen, entre Ninive et Chalé; c’est la grande ville. —
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Mesraïm engendra les Ludim, les Anamim, les Laabim, les Nephthuim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 les Phétrusim, les Chasluim, d’où sont sortis les Philistins, et les Caphtorim. —
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Canaan engendra Sidon, son premier-né, et Heth,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 ainsi que les Jébuséens, les Amorrhéens, les Gergéséens,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 les Hévéens, les Aracéens, les Sinéens,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 les Aradiens, les Samaréens et les Hamathéens. Ensuite les familles des Chananéens se répandirent dans le pays,
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 et le territoire des Chananéens alla depuis Sidon, dans la direction de Guérar, jusqu’à Gaza; et, dans la direction de Sodome, Gomorrhe, Adama, et Séboïm, jusqu’à Lésa. —
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Tels sont les fils de Cham selon leurs familles, selon leurs langues, dans leurs divers pays, dans leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Des fils naquirent aussi à Sem, qui est le père de tous les fils d’Héber et le frère aîné de Japheth.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Fils de Sem: Elam, Assur, Arphaxad, Lud et Aram. —
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Fils d’Aram: Us, Hul, Géther et Mes. —
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Arphaxad engendra Salé, et Salé engendra Héber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Et il naquit à Héber deux fils: le nom de l’un était Phaleg, parce que de son temps la terre était partagée, et le nom de son frère était Jectan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Jectan engendra Elmodad, Saleph, Asarmoth, Jaré,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 Aduram, Uzal, Décla,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 Ebal, Abimaël, Saba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 Ophir, Hévila et Jobab. Tous ceux-là sont fils de Jectan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Le pays qu’ils habitèrent fut la montagne d’Orient, à partir de Mésa, dans la direction de Séphar. —
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Tels sont les fils de Sem, selon leurs familles, selon leurs langues, dans leurs divers pays, selon leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Telles sont les familles des fils de Noé selon leurs générations, dans leurs nations. C’est d’eux que sont sorties les nations qui se sont répandues sur la terre après le déluge.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genèse 10 >