< Galates 4 >

1 Or je dis ceci: Aussi longtemps que l’héritier est enfant, il ne diffère en rien d’un esclave, quoiqu’il soit le maître de tout;
Ina cewa muddin magaji yaro ne, babu bambancin sa da bawa, ko da yake shine mai mallakan dukan kadarorin.
2 mais il est soumis à des tuteurs et à des curateurs jusqu’au temps marqué par le père.
A maimakon haka, yana karkashin masu jagora da amintattu har sai lokacin da mahaifinsa ya ajiye.
3 De même, nous aussi, quand nous étions enfants, nous étions sous l’esclavage des rudiments du monde.
Hakannan mu ma, lokaci da muke yara, an rike mu cikin kangi na tushin ka'idojin wannan duniya.
4 Mais lorsque est venue la plénitude des temps, Dieu a envoyé son Fils, formé d’une femme, né sous la Loi,
Amma da lokacin ya yi daidai, Allah ya aiko da dansa, haihuwar mace, haihuwar karkashin shari'a.
5 pour affranchir ceux qui sont sous la Loi, afin de nous conférer l’adoption.
Ya yi haka ne domin ya fanshi wadanda ke a karkashin shari'a, domin mu karbi diyanci a matsayin 'ya'ya.
6 Et parce que vous êtes fils, Dieu a envoyé dans vos cœurs l’Esprit de son Fils, lequel crie: Abba! Père!
Domin ku 'ya'ya ne, Allah ya aiko da Ruhun Dansa cikin zuciyarmu, Ruhun wanda ke kirar, “Abba, Uba.”
7 Ainsi tu n’es plus esclave, tu es fils; et si tu es fils, tu es aussi héritier, grâce à Dieu.
Saboda wannan dalilin kai ba kuma bawa ba ne amma da. Idan kai da ne, hakannan kuma kai ma magaji ne ta wurin Allah.
8 Autrefois, il est vrai, ne connaissant pas Dieu, vous serviez ceux qui par leur nature ne sont pas dieux;
Duk da haka a da, da ba ku san Allah ba, bayi ne ku ga alloli wadanda ainihi ba alloli ba ne ko kadan.
9 mais à présent que vous avez connu Dieu, ou plutôt que vous avez été connus de Dieu, comment retournez-vous à ces pauvres et faibles rudiments, auxquels de nouveau vous voulez vous asservir encore?
Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma, yanzu da Allah ya san ku, me ya sa kuke sake komawa zuwa ga tushen ka'idodin nan mara karfi da amfani? Kuna so ku sake komawa zaman bayi kuma daga farko?
10 Vous observez les jours, les mois, les temps et les années!
Kuna kiyaye ranaku na musamman, sabobin watanni, lokatai, da shekaru.
11 J’ai peur pour vous d’avoir travaillé en vain parmi vous.
Ina ji maku tsoro. Ina tsoro cewa kamar na yi aiki cikinku a wofi.
12 Devenez comme moi, puisque moi-même je suis comme vous, frères, je vous en supplie. Vous ne m’avez blessé en rien.
Ina rokon ku 'yan'uwa, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma na zama kamar ku. Ba ku yi mani laifin komai ba.
13 Quand je vous ai pour la première fois annoncé l’Evangile, vous savez quelle était l’infirmité de ma chair; et cependant ce qui dans ma chair était une épreuve pour vous,
Amma kun sani cewa saboda rashin lafiya ne na yi maku shelar bishara da farko.
14 vous ne l’avez ni méprisé ni repoussé; mais vous m’avez reçu comme un ange de Dieu, comme le Christ Jésus.
Ko da yake halin da nake ciki cikin jiki a zahiri ya sa ku cikin gwaji, ba ku raina ni ba ko kuma kuka watsar da ni. A maimakon haka, kun karbe ni kamar mala'ikan Allah, kamar ni Almasihu Yesu ne da kansa.
15 Que sont devenus ces heureux sentiments? Car je vous rends ce témoignage que, s’il eût été possible, vous vous seriez arraché les yeux pour me les donner.
Saboda haka, yanzu ina murnar taku? Domin ina shaidar ku, idan mai yiwuwa ne, da kun kwakulo idanunku, kun ba ni.
16 Je serais donc devenu votre ennemi, parce que je vous ai dit la vérité?
To kenan, na zama makiyin ku ne saboda na gaya maku gaskiya?
17 L’affection dont ces gens font étalage pour vous, n’est pas bonne, ils veulent vous détacher de nous, afin que vous vous attachiez à eux.
Suna neman ku da himma ba domin wani alheri ba ne. Suna so su raba ni da ku domin ku bi su.
18 Il est beau d’être l’objet d’une vive affection, quand c’est dans le bien, toujours, et non pas seulement quand je suis présent parmi vous.
Yana da kyau ko yaushe a yi himma domin dalilai masu kyau, ba kuma kawai sa'adda ina tare da ku ba.
19 Mes petits enfants, pour qui j’éprouve de nouveau les douleurs de l’enfantement, jusqu’à ce que le Christ soit formé en vous;
'Ya'yana kanana, sabili da ku ina cikin zafin nakuda kuma sai Almasihu ya samu kafuwa cikinku.
20 combien je voudrais être auprès de vous à cette heure et changer de langage, car je suis dans une grande perplexité à votre sujet!
Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canza muryata, domin ina damuwa a kanku kwarai.
21 Dites-moi, vous qui voulez être sous la Loi, n’entendez-vous pas la Loi?
Ku gaya mani, ku da kuke marmarin ku zo karkashin shari'a, ba ku ji abin da shari'ar ta ce ba?
22 Car il est écrit qu’Abraham eut deux fils, l’un de la servante, l’autre de la femme libre.
A rubuce yake cewa, Ibrahim yana da 'ya'ya maza biyu, daya dan baiwa ne, dayan kuma dan 'yantaciyar mace ne.
23 Mais le fils de la servante naquit selon la chair, et celui de la femme libre en vertu de la promesse.
Abin lura anan, dan baiwar an haife shi ta hanyar mutuntaka ne, amma dan 'yantaciyar macen, an haife shi ta wurin alkawari ne.
24 Ces choses ont un sens allégorique; car ces femmes sont deux alliances. L’une, du mont Sinaï, enfantant pour la servitude: c’est Agar,
Ana iya bayyana abubuwan nan a hanyar kwatanci kamar haka, wadannan mata na kama da alkawarai ne guda biyu. Dayan alkawarin daga dutsen Sinayi ne. Ta haifi 'ya'ya da ke bayi ne su. Ita ce Hajaratu.
25 — car Sinaï est une montagne en Arabie — elle correspond à la Jérusalem actuelle, laquelle est esclave, elle et ses enfants.
Yanzu fa, Hajaratu ita ce dutsen Sinayi da ke Arebiya. Misali ce na Urushalima na yanzu, domin tana cikin bauta tare da 'ya'yanta.
26 Mais la Jérusalem d’en haut est libre: c’est elle qui est notre mère;
Amma Urushalima da ke bisa 'yantacciya ce, ita ce mahaifiyarmu.
27 car il est écrit: « Réjouis-toi, stérile, toi qui n’enfantais point! Eclate en cris de joie et d’allégresse, toi qui ne connaissais pas les douleurs de l’enfantement! Car les enfants de la délaissée seront plus nombreux que les enfants de celle qui avait l’époux. »
Kamar yadda yake a rubuce, “Ki yi murna, ke bakarariya, ke da ba ki taba haihuwa ba. Ki yi shewa na farinciki, ke da ba ki dandana haihuwan da ba. Domin 'ya'yan bakarariya da yawa suke, fiye da ta mace mai miji.”
28 Pour vous, frères, vous êtes, à la manière d’Isaac, enfants de la promesse.
Yanzu fa, 'yan'uwa, kamar yadda Ishaku yake, haka muke, wato 'ya'yan alkawari.
29 Mais de même qu’alors celui qui était né selon la chair persécutait celui qui était né selon l’Esprit, ainsi en est-il encore maintenant.
A lokacin can, shi wanda aka haife shi ta hanyar mutuntaka ya tsananta wa wanda aka haife shi ta hanyar Ruhu. Haka yake har yanzu.
30 Mais que dit l’Ecriture? « Chasse l’esclave et son fils, car le fils de l’esclave ne saurait hériter avec le fils de la femme libre. »
Amma menene nassi ya ce? “Ka kori baiwar nan tare da danta. Domin dan baiwar nan ba za ya ci gado tare da dan macen nan da ke 'yantacciya ba.”
31 C’est pourquoi, frères, nous ne sommes pas enfants de la servante, mais de la femme libre.
Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan baiwa ba ne, a maimakon haka, mu 'ya'yan macen nan ne da ke 'yantacciya.

< Galates 4 >