< Ézéchiel 5 >

1 Et toi, fils de l’homme, prends une lame tranchante, prends-la en guise de rasoir de barbier, et fais-la passer sur ta tête et sur ta barbe; puis tu prendras des balances à peser, et tu partageras ce que tu auras coupé.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 Tu en brûleras un tiers dans le feu, au milieu de la ville, lorsque les jours du siège seront accomplis; tu en prendras un tiers que tu frapperas avec l’épée autour de la ville; et l’autre tiers, tu le disperseras au vent, et je tirerai l’épée derrière eux.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 Et tu en prendras une petite quantité, que tu serreras dans les ailes de ton vêtement.
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 De ce reste, tu en prendras encore pour le jeter au milieu du feu, et tu le brûleras dans le feu. De là sortira un feu pour toute la maison d’Israël.
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 Ainsi parle le Seigneur Yahweh: C’est là cette Jérusalem que j’avais placée au milieu des nations, avec de vastes contrées autour d’elle!
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 Mais, dans sa méchanceté, elle à résisté à mes décrets plus que les nations, et à mes lois plus que les pays qui l’entourent; car ils ont rejeté mes décrets et n’ont pas marché suivant mes lois.
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 C’est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Parce que vous avez été plus rebelles que les nations qui vous entourent, que vous n’avez pas marché suivant mes lois, que vous n’avez pas observé mes décrets et que vous n’avez pas agi selon les coutumes des nations qui vous entourent,
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 à cause de cela le Seigneur Yahweh parle ainsi: Voici que je viens contre toi à mon tour! Moi, j’exécuterai des décrets au milieu de toi sous les yeux des nations;
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 et je ferai contre toi une chose telle que je n’en ai pas fait et que je n’en ferai jamais plus de pareille, — à cause de toutes tes abominations.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 C’est pourquoi des pères dévoreront leurs fils au milieu de toi, et des fils dévoreront leurs pères. J’exécuterai contre toi des jugements, et je disperserai à tout vent tout ce qui restera de toi.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 C’est pourquoi, je suis vivant, oracle du Seigneur Yahweh: Parce que tu as souillé mon sanctuaire par toutes tes infamies et toutes tes abominations, moi aussi je briserai, et mon œil sera sans pitié, et je n’aurai pas de compassion.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 Un tiers de tes enfants mourra par la peste et sera consumé par la famine au milieu de toi; un tiers tombera par l’épée tout autour de toi; et, pour l’autre tiers, je le disperserai à tout vent, et je tirerai l’épée derrière eux.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 Et ma colère s’assouvira, et j’apaiserai mon courroux sur eux et je serai satisfait; et ils sauront que moi, Yahweh, j’ai parlé dans ma jalousie, quand j’aurai assouvi sur eux mon courroux.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 Je te livrerai à l’opprobre et à la désolation parmi les nations qui t’entourent, aux yeux de tous les passants.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 Tu seras un opprobre et une honte, une leçon et un sujet de terreur pour les peuples qui t’entourent, quand j’exécuterai sur toi des jugements avec colère, avec courroux, et par les châtiments de mon courroux, — c’est moi, Yahweh, qui parle! —
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 quand je décocherai sur eux les flèches funestes de la famine, qui servent à détruire et que je lancerai sur vous pour vous détruire; car j’augmenterai encore pour vous la famine, et je briserai pour vous le bâton du pain;
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 et j’enverrai sur vous la famine et des bêtes malfaisantes, qui te priveront d’enfants; la peste et le sang passeront sur toi, et je ferai venir sur toi l’épée — moi, Yahweh, j’ai parlé!
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Ézéchiel 5 >