< Ézéchiel 26 >
1 La onzième année, le premier du mois, la parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma sha ɗaya, a rana ta fari ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 « Fils de l’homme, parce que Tyr a dit de Jérusalem: Ha! Ha! elle est brisée, la porte des peuples! on se tourne vers moi; je vais me remplir! elle est devenue un désert! —
“Ɗan mutum, domin Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Yauwa! Ƙofar zuwa al’ummai ta karye, an kuma buɗe mini ƙofofinta; yanzu da take kufai zan wadace,’
3 à cause de cela ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je viens contre toi, Tyr! Je vais faire monter contre toi des nations nombreuses, comme la mer fait monter ses flots.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da ke, ya Taya, zan kuwa kawo al’ummai masu yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa.
4 Elles détruiront les murs de Tyr, et abattront ses tours; je balaierai loin d’elle sa poussière, et je ferai d’elle un rocher nu.
Za su hallaka katangar Taya su kuma rurrushe hasumiyoyinta; zan kankare tarkacenta, in maishe ta fā.
5 Elle sera, au milieu de la mer, un lieu où l’on étend les filets; car moi j’ai parlé, — oracle du Seigneur Yahweh; elle sera la proie des nations.
Za tă zama wurin shanya abin kamun kifi a tsakiyar teku, gama na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Za tă zama ganima ga sauran al’ummai,
6 Ses filles qui sont sur la terre ferme seront tuées par l’épée, et on saura que je suis Yahweh.
za a kashe mazaunan filin ƙasar da takobi. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.
7 Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je vais amener du septentrion contre Tyr, Nabuchodonosor, roi de Babylone, le roi des rois, avec des chevaux, des chars, des cavaliers, et une multitude de troupes et un peuple nombreux.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa daga arewa zan kawo wa Taya Nebukadnezzar sarkin Babilon, sarkin sarakuna, tare da dawakai da kekunan yaƙi, da mahayan dawakai da babbar rundunar soja.
8 Il tuera par l’épée tes filles sur la terre ferme, il construira contre toi des murs, il élèvera contre toi des terrasses, et dressera contre toi la tortue.
Zai kashe mazaunan filin ƙasar da takobi; zai yi miki ƙawanya, ya gina miki mahaurai, sa’an nan ya rufe ki da garkuwoyi.
9 Il dirigera contre tes murs le choc de ses béliers, et démolira tes tours avec ses crochets.
Zai rushe katangarki da dundurusai, ya rurrushe hasumiyoyinki da makamai.
10 Telle sera la multitude de ses chevaux que leur poussière te couvrira; au bruit des cavaliers, des roues et des chars, tes murs trembleront, quand il entrera dans tes portes, comme on entre dans une ville forcée.
Dawakansa za su yi yawa har su rufe ke da ƙura. Katanga za su girgiza saboda motsin dawakan yaƙi, kekunan doki da keken yaƙin sa’ad da suka shiga birnin da aka rushe katangar.
11 Du sabot de ses chevaux, il foulera toutes les rues; il tuera ton peuple par l’épée, et tes puissantes colonnes seront jetées par terre.
Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki; zai kashe mutanenki da takobi, ginshiƙanki masu ƙarfi kuma za su fāɗi a ƙasa.
12 Ils enlèveront tes richesses, pilleront tes marchandises, abattront tes murailles, renverseront tes beaux palais, et jetteront au milieu des eaux tes pierres, ton bois et ta poussière.
Za su washe dukiyarki, kayan cinikinki kuma su zama ganima; za su rurrushe katangarki su ragargaza gidajenki masu kyau su kuma zubar da duwatsunki, katakanki da kuma tarkacenki a cikin teku.
13 Je ferai cesser le bruit de tes chansons, et le son de tes cithares ne se fera plus entendre.
Zan kawo ƙarshen waƙoƙinki masu surutu, ba kuwa za a ƙara jin kaɗe-kaɗen garayunki ba.
14 Je ferai de toi un rocher nu, tu seras un lieu où l’on étend les filets; tu ne seras plus rebâtie; car moi, Yahweh, j’ai parlé, — oracle du Seigneur Yahweh.
Zan maishe ki fā, za ki kuma zama wurin shanya abin kamun kifi. Ba za a sāke gina ki ba, gama Ni Ubangiji na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Ainsi parle à Tyr le Seigneur Yahweh: Au bruit de ta chute, quand tes blessés pousseront des gémissements, quand le carnage sévira au milieu de toi, les îles ne trembleront-elles pas?
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Taya. Ƙasashen da suke a bakin teku ba za su girgiza saboda ƙarar fāɗuwarki, sa’ad da nishin waɗanda aka yi wa rauni da kashe-kashen da aka yi a cikinki suka faru ba?
16 Et ils descendront de leurs trônes, tous les princes de la mer; ils quitteront leurs manteaux, et déposeront leurs vêtements brodés; ils se vêtiront d’épouvante, ils s’assoieront sur la terre; ils trembleront à chaque moment, et seront dans la stupeur à cause de toi.
Sa’an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci suna razana saboda abin da ya same ki.
17 Et ils prononceront sur toi une complainte, et ils te diront: « Comment as-tu péri, toi qui te dressais au sein des mers, ô toi ville célèbre, qui étais puissante sur la mer, toi et tes habitants, alors qu’ils inspiraient la terreur à tous les habitants de la mer. »
Sa’an nan za su yi makoki game da ke su ce, “‘Yaya kika hallaka haka nan, ya birnin da ta yi suna, cike da mutanen teku! Ke da kika zama mai ƙarfi cikin tekuna, ke da mazauna cikinki; kin sa tsoronki a kan dukan waɗanda suka zauna a can.
18 Maintenant les îles trembleront au jour de ta chute, et les îles qui sont dans la mer seront épouvantées de ta fin.
Yanzu tsibirai suna rawar jiki a ranar fāɗuwarki; tsibirai a cikin teku sun tsorata a ɓacewarki.’
19 Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: Quand j’aurai fait de toi une ville déserte, comme les villes qui n’ont pas d’habitants; quand j’aurai fait monter sur toi l’abîme, et que les grandes eaux t’auront couverte,
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na maishe ki kufai, kamar sauran biranen da ba a ƙara zama a ciki, sa’ad da kuma na kawo zurfafan teku a kanki da yawan ruwansa suka rufe ki,
20 je te ferai descendre avec ceux qui sont descendus dans la fosse, vers les peuples d’autrefois; je te ferai habiter dans les profondeurs de la terre, dans les solitudes éternelles, avec ceux qui sont descendus dans la fosse, pour que tu ne sois plus habitée; et je mettrai un ornement sur la terre des vivants.
a sa’an nan zan sauko da ke ƙasa tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna ƙarƙashin ƙasa, kamar a kufai na tun dā, tare da waɗanda suke gangarawa zuwa rami, ba kuwa za ki ƙara dawowa ba ko ki ɗauki matsayinki a ƙasar masu rai.
21 Je ferai de toi un objet d’épouvante, et tu ne seras plus; on te cherchera, et on ne te trouvera plus jamais, — oracle du Seigneur Yahweh. »
Zan sa ki yi mummunan ƙarshe kuma ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a ƙara same ki ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”