< Ézéchiel 16 >

1 La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 « Fils de l’homme, fais connaître à Jérusalem ses abominations
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 et dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh, à Jérusalem: Par ton origine et ta naissance, tu es de la terre du Chananéen; ton père était l’Amorrhéen et ta mère une Hittitene.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 Quant à ta naissance, le jour où tu naquis, ton cordon n’a pas été coupé, et tu n’as pas été baignée dans l’eau pour être purifiée; tu n’as pas été frottée de sel, ni enveloppée de langes.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Aucun œil n’eut pitié de toi pour te rendre un seul de ces soins, par compassion pour toi; mais on te jeta, par dégoût de toi, sur la face des champs, le jour de ta naissance.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 Je passai près de toi et je te vis te débattant dans ton sang, et je te dis: Vis dans ton sang.
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Je te fis multiplier comme l’herbe des champs; tu te multiplias et tu grandis; tu acquis une beauté parfaite; tes seins se formèrent et tu arrivas à la puberté; mais tu étais nue, entièrement nue.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Et je passai près de toi et je te vis; et voici que ton temps était venu, le temps des amours; j’étendis sur toi le pan de mon manteau et je couvris ta nudité; je te fis un serment et j’entrai en alliance avec toi, — oracle du Seigneur Yahweh, — et tu fus à moi.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Je te baignai dans l’eau, et je lavai ton sang de dessus toi, et je t’oignis d’huile.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Je te vêtis de broderie, et je te chaussai de peau de veau marin; je ceignis ta tête d’un voile de lin, et je te couvris de soie.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Je t’ornai d’une parure: je mis des bracelets à tes mains, et un collier à ton cou;
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 je mis à ton nez un anneau, des boucles à tes oreilles, et sur ta tête un magnifique diadème.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Tu t’ornas d’or et d’argent, et tu fus vêtue de lin, de soie et de broderie; la fleur de froment, le miel et l’huile étaient ta nourriture; tu devins extraordinairement belle, et tu arrivas à la dignité royale.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Ton nom se répandit parmi les nations à cause de ta beauté; car elle était parfaite, grâce à ma splendeur que j’avais répandue sur toi, — oracle du Seigneur Yahweh.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Mais tu mis ta confiance en ta beauté, et tu te prostituas à la faveur de ton nom; tu prodiguas tes amours à tout passant, te livrant à lui.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Et tu as pris de tes vêtements, et tu t’en es fait des hauts lieux aux couleurs variées, et tu t’es prostituée dessus: ce qui ne s’était jamais fait et ne se fera jamais.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Tu as pris tes bijoux, faits de mon or et de mon argent que je t’avais donnés, et tu t’en es fait des images d’hommes, auxquelles tu t’es prostituée.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Tu as pris tes vêtements brodés et tu les en as couvertes, et tu as mis devant elles mon huile et mon encens.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Mon pain que je t’avais donné, la fleur de froment, l’huile et le miel dont je te nourrissais, tu les as mis devant elles en offrande d’agréable odeur. Voilà ce qui s’est fait, — oracle du Seigneur Yahweh.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Tu as pris tes fils et tes filles que tu m’avais enfantés; tu les leur a offerts en sacrifice pour qu’ils les dévorassent. Etait-ce trop peu de tes prostitutions,
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 que tu aies égorgé mes fils, et que tu les leur aies livrés, en les faisant passer par le feu en leur honneur?
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Et au milieu de toutes tes abominations et de tes prostitutions, tu ne t’es pas souvenue des jours de ta jeunesse, quand tu étais nue, complètement nue, te débattant dans ton sang.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Après toutes tes méchantes actions, — malheur, malheur à toi! oracle du Seigneur Yahweh —
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 tu t’es construit une voûte et tu t’es fait un tertre sur toutes les places.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 A chaque carrefour tu as élevé ton tertre; tu as souillé ta beauté; tu t’es livrée à tout passant, tu as multiplié tes prostitutions.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Tu t’es prostituée aux fils de l’Égypte, tes voisins, aux membres vigoureux, et tu as multiplié tes prostitutions pour m’irriter.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Et voici que j’ai étendu ma main sur toi; j’ai diminué ta portion; je t’ai livrée au bon plaisir de tes ennemies, les filles des Philistins, qui ont rougi de ta conduite criminelle.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Et tu t’es prostituée aux fils d’Assur, parce que tu n’étais pas rassasiée; et, après t’être prostituée à eux, tu n’as pas encore été rassasiée.
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Et tu as multiplié tes prostitutions dans le pays de Canaan jusqu’en Chaldée, et avec cela tu n’as pas encore été rassasiée.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Oh! que ton cœur est faible, — oracle du Seigneur Yahweh, — pour que tu aies fait toutes ces choses, ce que fait la prostituée la plus dévergondée!
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 Quand tu construisais ta voûte à chaque carrefour et que tu faisais ton tertre à chaque place, tu n’étais pas comme la prostituée, car tu dédaignais le salaire;
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 tu étais la femme adultère, qui prend des étrangers à la place de son mari.
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 A toutes les prostituées on donne des présents; mais toi, tu as donné tes présents à tous tes amants, tu les as payés, pour qu’ils viennent vers toi, de toutes parts, pour tes prostitutions.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Il t’est arrivé, dans tes prostitutions, le contraire de ce qui arrive aux autres femmes: personne ne te recherchait. En donnant des présents alors qu’on ne t’en faisait pas, tu as été au rebours des autres.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 C’est pourquoi, prostituée, écoute la parole de Yahweh:
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Parce que ton airain a été répandu et que ta nudité a été découverte, dans tes prostitutions avec tes amants et avec toutes tes abominables idoles, et à cause du sang de tes enfants que tu leur as donnés,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 à cause de cela voici que je rassemblerai tous tes amants avec lesquels tu as eu commerce, tous ceux que tu as aimés, avec tous ceux que tu as haïs; je vais les rassembler contre toi de toutes parts; je découvrirai ta nudité devant eux, et ils verront toute ta nudité.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Je te jugerai selon le droit des femmes adultères et de celles qui répandent le sang; et je ferai de toi une victime sanglante de fureur et de jalousie.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Je te livrerai entre leurs mains; ils abattront ta voûte et démoliront tes hauts lieux; ils te dépouilleront de tes vêtements, prendront tes bijoux et te laisseront nue, complètement nue.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Ils feront monter contre toi une assemblée; ils te lapideront et te perceront de leurs épées.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Ils brûleront tes maisons par le feu et ils exécuteront contre toi des jugements, sous les yeux de beaucoup de femmes; je ferai cesser tes prostitutions, et tu ne feras plus de présents.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 J’assouvirai sur toi mon courroux, et ma jalousie s’éloignera de toi; je m’apaiserai et ne serai plus irrité.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Parce que tu ne t’es pas souvenue des jours de ta jeunesse et que tu m’as irrité par tous ces excès, voici que moi, à mon tour, je ferai retomber ta conduite sur ta tête, — oracle du Seigneur Yahweh; et tu ne commettras plus l’impudicité avec toutes tes abominations.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Voici que tous ceux qui disent des proverbes en feront à ton sujet en disant:
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Telle mère, telle fille! Tu es bien la fille de ta mère qui a rejeté son mari et ses enfants, et tu es la sœur de tes sœurs qui ont rejeté leurs maris et leurs enfants; votre mère est une Hittitene, et votre père un Amorrhéen.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Ta grande sœur, qui demeure à ta gauche, c’est Samarie avec ses filles; et ta petite sœur, qui demeure à ta droite, c’est Sodome avec ses filles.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Tu n’as pas seulement marché dans leurs voies et agi selon leurs abominations: c’était trop peu; tu t’es corrompue plus qu’elles dans toutes tes voies.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Je suis vivant, — oracle du Seigneur Yahweh: Sodome, ta sœur, elle et ses filles, n’ont pas fait ce que tu as fait, toi, et tes filles.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Voici quel fut le crime de Sodome, ta sœur: l’orgueil, l’abondance et l’insouciant repos où elle vivait avec ses filles, et elle ne soutenait pas la main du malheureux et de l’indigent.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Elles sont devenues orgueilleuses, et elles ont commis l’abomination devant moi, et je les ai fait disparaître quand j’ai vu cela.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Samarie n’a pas commis la moitié de tes péchés; tu as multiplié tes abominations plus qu’elles ne l’avaient fait, et tu as justifié tes sœurs par toutes tes abominations que tu as commises.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Porte donc, toi aussi, ton opprobre, que tu rejetais sur tes sœurs, à cause de tes péchés par lesquels tu t’es rendue plus abominable qu’elles; elles sont plus justes que toi. Toi aussi, sois couverte de confusion et porte ton opprobre, puisque tu as justifié tes sœurs.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Je ramènerai leurs captifs, les captifs de Sodome et de ses filles, les captifs de Samarie et de ses filles, et tes captifs parmi les leurs,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 afin que tu portes ton opprobre et que tu sois confuse de tout ce que tu as fait pour les consoler.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Ta sœur Sodome et ses filles reviendront à leur premier état, Samarie et ses filles reviendront à leur premier état; et toi et tes filles, vous reviendrez à votre premier état.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Ta sœur Sodome n’était pas nommée par ta bouche aux jours de ton orgueil,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 avant que ta perversité fut mise à nu, comme au temps où tu fus outragée par les filles de la Syrie et de tous ses alentours, par les filles des Philistins qui t’insultaient autour de toi.
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Ton crime et tes abominations, tu en as porté la peine, — oracle de Yahweh.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Car ainsi parle le Seigneur Yahweh: J’agirai avec toi comme tu as agi, toi qui as méprisé ton serment en rompant l’alliance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Mais moi, je me souviendrai de mon alliance que j’ai contractée avec toi aux jours de ta jeunesse, et j’établirai avec toi une alliance éternelle.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Tu te souviendras de ta conduite et tu en auras honte, quand tu recevras tes sœurs, celles qui sont plus grandes que toi avec celles qui sont plus petites que toi, et que je te les donnerai pour filles, mais non en vertu de ton alliance.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 J’établirai mon alliance avec toi, et tu sauras que je suis Yahweh,
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 afin que tu te souviennes et que tu rougisses, afin que tu n’ouvres plus la bouche à cause de ta confusion, quand je ferai l’expiation pour toi, pour tout ce que tu as fait, — oracle du Seigneur Yahweh. »
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ézéchiel 16 >