< Exode 23 >

1 Tu ne sèmeras pas de faux bruit; tu ne donneras pas la main à un méchant en lui servant de témoin à charge.
“Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
2 Tu ne suivras pas la multitude pour faire le mal, et tu ne déposeras pas dans un procès en te mettant du côté du grand nombre pour faire fléchir la justice.
“Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
3 Tu ne favoriseras pas non plus un faible dans son procès.
Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
4 Si tu rencontres le bœuf de ton ennemi ou son âne égaré, tu ne manqueras pas de le lui ramener.
“In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
5 Si tu vois l’âne de celui qui te hait succombant sous sa charge, tu te garderas de l’abandonner; joins tes efforts aux siens pour le décharger.
In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
6 Tu ne feras pas fléchir le droit du pauvre dans son procès.
“Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
7 Tu t’éloigneras d’une cause mensongère, et tu ne feras pas mourir l’innocent et le juste; car je n’absoudrai pas un coupable.
Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
8 Tu n’accepteras pas de présents; car les présents aveuglent les clairvoyants et ruinent les causes justes.
“Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
9 Tu n’opprimeras pas l’étranger; vous savez ce que ressent l’étranger, car vous avez été étrangers dans le pays d’Égypte.
“Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
10 Pendant six années tu ensemenceras ta terre et tu en récolteras les produits.
“Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
11 Mais, la septième, tu les laisseras et les abandonneras; et les indigents de ton peuple les mangeront, et les bêtes des champs mangeront ce qui restera. Tu feras de même pour tes vignes et les oliviers.
amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
12 Pendant six jours tu feras ton ouvrage; mais le septième jour tu te reposeras, afin que ton bœuf et ton âne aient du repos, et que le fils de ta servante et l’étranger respirent.
“Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
13 Vous prendrez garde à tout ce que je vous ai dit; vous ne prononcerez pas le nom de dieux étrangers, et on n’en entendra pas sortir de votre bouche.
“Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
14 Trois fois chaque année tu célébreras une fête en mon honneur.
“Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
15 Tu observeras la fête des Azymes: pendant sept jours tu mangeras des pains sans levain, comme je t’en ai donné l’ordre, au temps fixé, au mois d’abib, car c’est dans ce mois que tu es sorti d’Égypte; et l’on ne se présentera pas les mains vides devant ma face.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
16 Tu observeras la fête de la Moisson, des prémices de ton travail, de ce que tu auras semé dans les champs; et la fête de la Récolte, à la fin de l’année, quand tu recueilleras des champs le fruit de ton travail.
“Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
17 Trois fois l’année, tous tes mâles se présenteront devant le seigneur Yahweh.
“Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
18 Tu n’offriras pas avec du pain levé le sang de ma victime, et la graisse de ma fête ne sera pas gardée pendant la nuit jusqu’au matin.
“Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
19 Tu apporteras les prémices des premiers fruits de ton sol à la maison de Yahweh, ton Dieu. Tu ne feras pas cuire un chevreau dans le lait de sa mère.
“Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
20 Voici que j’envoie un ange devant toi, pour te garder dans le chemin et pour te faire arriver au lieu que j’ai préparé.
“Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
21 Sois sur tes gardes en sa présence et écoute sa voix; ne lui résiste pas, car il ne pardonnerait pas votre transgression, parce que mon nom est en lui.
Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
22 Mais si tu écoutes sa voix, et si tu fais tout ce que je dirai, je serai l’ennemi de tes ennemis et l’adversaire de tes adversaires.
In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
23 Car mon ange marchera devant toi et te conduira vers les Amorrhéens, les Hittites, les Phérézéens, les Chananéens, les Hévéens et les Jébuséens, et je les exterminerai.
Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
24 Tu n’adoreras pas leurs dieux et tu ne les serviras pas; tu ne les imiteras pas dans leurs pratiques, mais tu renverseras et briseras leurs stèles.
Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
25 Vous servirez Yahweh, votre Dieu, et il bénira ton pain et ton eau, et j’éloignerai la maladie du milieu de toi.
Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
26 Il n’y aura dans ton pays ni femme qui perde son fruit, ni femme stérile; je remplirai le nombre de tes jours.
A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
27 J’enverrai ma terreur devant toi, je jetterai dans la confusion tous les peuples chez lesquels tu arriveras, et je ferai tourner le dos devant toi à tous tes ennemis.
“Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
28 J’enverrai devant toi les frelons, qui chasseront loin de ta face les Hévéens, les Chananéens et les Hittites.
Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
29 Je ne les chasserai pas de ta face en une seule année, de peur que le pays ne devienne un désert, et que les bêtes sauvages ne se multiplient contre toi.
Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
30 Je les chasserai peu à peu de devant toi, jusqu’à ce que tu augmentes en nombre et que tu puisses occuper le pays.
Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
31 J’établirai tes limites depuis la mer Rouge jusqu’à la mer des Philistins, et depuis le désert jusqu’au fleuve; car je livrerai entre vos mains les habitants du pays, et tu les chasseras de devant toi.
“Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
32 Tu ne feras pas alliance avec eux, ni avec leurs dieux.
Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
33 Ils n’habiteront pas dans ton pays, de peur qu’ils ne te fassent pécher contre moi; tu servirais leurs dieux, et ce serait un piège pour toi. »
Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”

< Exode 23 >