< Ecclésiaste 9 >

1 En effet, j’ai pris tout ceci à cœur, et j’ai observé tout ceci: Que les justes et les sages et leurs œuvres sont dans la main de Dieu; l’homme ne connaît ni l’amour, ni la haine: tout est devant eux.
Sai na yi tunani a kan wannan na kuma gane cewa masu adalci da masu hikima da kuma abubuwan da suke yi suna a hannun Allah ne, amma ba wanda ya san ko ƙauna ko ƙiyayya ce take jiransa.
2 Tout arrive également à tous: même sort pour le juste et pour le méchant, pour celui qui est bon et pur, et pour celui qui est impur, pour celui qui sacrifie et pour celui qui ne sacrifie pas. Comme il arrive à l’homme bon, il arrive au pécheur; il en est de celui qui jure comme de celui qui craint de jurer.
Dukansu makomarsu ɗaya ce, masu adalci da masu mugunta, masu kirki da marasa kirki, masu tsabta da marasa tsabta, masu miƙa hadaya da waɗanda ba sa yi. Kamar yadda yake ga mutumin kirki, haka yake ga mai zunubi. Kamar yadda yake ga masu yin rantsuwa, haka ma da masu tsoron yi.
3 C’est un mal, parmi tout ce qui se fait sous le soleil, qu’il y ait pour tous un même sort; c’est pourquoi le cœur des fils de l’homme est plein de malice, et la folie est dans leur cœur pendant leur vie; après quoi ils vont chez les morts.
Wannan ita ce muguntar da take faruwa a cikin dukan abubuwa a duniya. Ƙaddara ɗaya ce take a kan kowa. Amma zukatan mutane cike suke da mugunta, akwai kuma hauka a zukatansu yayinda suke a raye, bayan haka kuma sai su mutu.
4 Car pour l’homme qui est parmi les vivants, il y a de l’espérance; mieux vaut un chien vivant qu’un lion mort.
Duk wanda yake da rai a wannan duniya ta rayayyu, yana sa zuciya, gara rayayyen kare da mataccen zaki!
5 Les vivants, en effet, savent qu’ils mourront, mais les morts ne savent rien, et il n’y a plus pour eux de salaire; car leur mémoire est oubliée.
Gama rayayyu sun san za su mutu, amma matattu ba su san kome ba; ba su da wata lada nan gaba an manta da su ke nan gaba ɗaya.
6 Déjà leur amour, leur haine, leur envie ont péri, et ils n’auront plus jamais aucune part à ce qui se fait sous le soleil.
Ƙaunarsu, ƙiyayyarsu, da kuma kishinsu tuni sun ɓace; ba za su taɓa zama sashen wani abin da yake faruwa a duniya ba.
7 Va, mange avec joie ton pain et bois ton vin d’un cœur content, puisque déjà Dieu se montre favorable à tes œuvres.
Yi tafiyarka, ka ci abincinka da farin ciki, ka sha ruwan inabinka da farin zuciya, gama abin da ka yi duka daidai ne a wurin Allah.
8 Qu’en tout temps tes vêtements soient blancs, et que l’huile parfumée ne manque pas sur ta tête.
Kullum ka kasance cikin farin riguna, ka kuma shafe kanka da mai kullum,
9 Jouis de la vie avec une femme que tu aimes, pendant tous les jours de ta vie de vanité que Dieu t’a donnée sous le soleil, pendant tous les jours de ta vanité; car c’est ta part dans la vie et dans le travail que tu fais sous le soleil.
Ka more rayuwa da matarka, wadda kake ƙauna, dukan kwanakin nan marasa amfani da Allah ya ba ka a duniya. Gama wannan ne rabonka a rayuwa da kuma na faman aikinka a duniya.
10 Tout ce que ta main peut faire, fais-le avec ta force; car il n’y a plus ni œuvre, ni intelligence, ni science, ni sagesse, dans le schéol où tu vas. (Sheol h7585)
Duk abin da hannunka yake yi, ka yi shi da dukan ƙarfinka, gama a cikin kabari in da za ka, babu aiki ko shirye-shirye, ko sani, ko hikima. (Sheol h7585)
11 Je me suis tourné et j’ai vu sous le soleil que la course n’est pas aux agiles, ni la guerre aux vaillants, ni le pain aux sages, ni la richesse aux intelligents, ni la faveur aux savants; car le temps et les accidents les atteignent tous.
Na kuma ga wani abu a duniya. Ba kullum maguji ne yake nasara a tsere ba, ba kullum jarumi ne yake yin nasara ba, ba kullum mai hikima ne da abinci ba ba kullum mai basira ne yake da wadata ba ba kullum gwani ne yake samun tagomashi ba; amma sa’a, da tsautsayi, sukan sami kowannensu.
12 Car l’homme ne connaît même pas son heure, pareil aux poissons qui sont pris au filet fatal, pareil aux oiseaux qui sont pris au piège; comme eux les enfants des hommes sont enlacés au temps du malheur, quand il fond sur eux tout à coup.
Ban da haka ma, ba wanda ya san sa’ad da lokacin mutuwarsa zai yi. Kamar yadda akan kama kifi a muguwar raga, ko a kama tsuntsu a tarko, haka mugun lokaci yakan auko wa mutane, ba tsammani.
13 J’ai encore vu sous le soleil ce trait de sagesse, et celle-ci m’a paru grande.
Na kuma ga wani misali game da hikima a duniya wanda ya burge ni sosai.
14 Il y avait une petite ville, avec peu d’hommes dans ses murs; un roi puissant vint contre elle, l’investit, et bâtit contre elle de hautes tours.
An yi wani ɗan ƙaramin birni mai mutane kaɗan a ciki. Sai wani babban sarki ya kawo masa yaƙi, ya kafa masa babban sansani.
15 Et il s’y trouva un homme pauvre et sage, qui sauva la ville par sa sagesse. Et personne ne s’est souvenu de cet homme pauvre.
A cikin birnin nan kuwa akwai wani mutum matalauci amma mai hikima, ya kuma ceci birnin ta wurin hikimarsa. Amma ba wanda ya tuna da matalaucin nan.
16 Et j’ai dit: « La sagesse vaut mieux que la force; mais la sagesse du pauvre est méprisée, et ses paroles ne sont pas écoutées. »
Sai na ce, “Hikima ta fi ƙarfe ƙarfi.” Amma aka rena hikimar matalaucin, ba a ma jin maganarsa.
17 Les paroles des sages, prononcées avec calme, sont écoutées, mieux que les cris d’un chef au milieu des insensés.
Raɗar mai hikima da aka saurara cikin natsuwa ta fi ihun mai mulkin wawaye.
18 La sagesse vaut mieux que des instruments de guerre; mais un seul pécheur peut détruire beaucoup de bien.
Hikima ta fi kayan yaƙi, amma mai zunubi ɗaya yakan rushe alheri mai yawa.

< Ecclésiaste 9 >