< Ecclésiaste 7 >

1 Une bonne renommée vaut mieux qu’un bon parfum, et le jour de la mort que le jour de la naissance.
Suna mai kyau ya fi turare mai ƙanshi, kuma ranar mutuwa ta fi ranar haihuwa.
2 Mieux vaut aller à la maison de deuil qu’aller à la maison de festin, car dans la première apparaît la fin de tout homme, et le vivant y applique son cœur.
Gara a tafi gidan makoki da a je gidan biki, gama mutuwa ce ƙaddarar kowane mutum; ya kamata masu rai su lura da haka.
3 Mieux vaut la tristesse que le rire, car un visage triste fait du bien au cœur.
Baƙin ciki ya fi dariya, gama baƙin ciki yakan kawo gyara.
4 Le cœur des sages est dans la maison de deuil, et le cœur des insensés dans la maison de joie.
Zuciyar masu hikima tana a gidan makoki, amma zuciya wawaye tana a gidan shagali.
5 Mieux vaut entendre la réprimande du sage que d’entendre la chanson des insensés.
Gara ka saurari tsawatawar mai hikima da ka saurari waƙar wawaye.
6 Car semblable au pétillement des épines sous la chaudière est le rire des insensés: c’est là encore une vanité.
Kamar ƙarar ƙayar da take karce gindin tukunya, haka dariyar wawaye take. Wannan ma ba shi da amfani.
7 Car l’oppression rend insensé le sage, et les présents corrompent le cœur.
Zalunci yakan mai da mutum mai hikima wawa, cin hanci kuma yakan lalace hali.
8 Mieux vaut la fin d’une chose que son commencement; mieux vaut un esprit patient qu’un esprit hautain.
Ƙarshen abu ya fi farkonsa, haƙuri kuma ya fi girman kai.
9 Ne te hâte pas dans ton esprit de t’irriter, car l’irritation repose dans le sein des insensés.
Kada ranka yă yi saurin tashi, gama fushi yana zama a cinyar wawaye.
10 Ne dis pas: « D’où vient que les jours anciens étaient meilleurs que ceux-ci? » Car ce n’est pas par sagesse que tu interroges à ce sujet.
Kada ka ce, “Me ya sa kwanakin dā sun fi waɗannan?” Gama ba daidai ba ne a yi irin waɗannan tambayoyi.
11 La sagesse est bonne avec un patrimoine, et profitable à ceux qui voient le soleil.
Hikima, kamar gādo, abu mai kyau ne tana kuma da amfani ga waɗanda suka ga rana.
12 Car telle la protection de l’argent, telle la protection de la sagesse; mais un avantage du savoir, c’est que la sagesse fait vivre ceux qui la possèdent.
Hikima mafaka ce takan kāre mutum kamar yadda kuɗi suke yi. Kiyayewar da hikima takan yi wa mai ita ita ce amfanin ilimi.
13 Regarde l’œuvre de Dieu: qui pourra redresser ce qu’il a courbé?
Ku lura da abin da Allah ya yi. Wa zai iya miƙe abin da ya tanƙware?
14 Au jour du bonheur, sois joyeux, et au jour du malheur, réfléchis: Dieu a fait l’un comme l’autre, afin que l’homme ne découvre pas ce qui doit lui arriver.
Sa’ad da al’amura suke tafiya daidai, ka yi farin ciki, amma sa’ad da suka lalace, ka tuna, Allah ne ya yi wancan shi ne kuma ya yi wannan. Saboda haka, mutum ba zai san wani abu game da nan gabansa ba.
15 Tout ceci, je l’ai vu au jour de ma vanité: il y a tel juste qui périt dans sa justice, et il y a tel méchant qui prolonge sa vie dans sa méchanceté.
A cikin rayuwan nan ta rashin amfani nawa, na lura da waɗannan abubuwa biyu, mai adalci yana hallakawa cikin adalcinsa, mai mugunta kuma yana tsawon rai cikin muguntarsa.
16 Ne sois pas juste à l’excès, et ne te montre pas sage outre mesure: pourquoi voudrais-tu te détruire?
Kada ka cika yin adalci, fiye da kima, kada kuma ka cika yin hikima, don me za ka hallaka kanka!
17 Ne sois pas méchant à l’excès, et ne sois pas insensé: pourquoi voudrais-tu mourir avant ton temps?
Kada ka cika yin mugunta, kada kuma ka cika yin wauta, don me za ka mutu kafin lokacinka?
18 Il est bon que tu retiennes ceci, et que tu ne relâches pas ta main de cela, car celui qui craint Dieu évite tous ces excès.
Yana da kyau ka kama ɗaya ba tare da ka saki wancan ba. Mai tsoron Allah zai guji wuce gona da iri.
19 La sagesse donne au sage plus de force que n’en possèdent dix chefs qui sont dans la ville.
Hikima takan sa mutum guda mai hikima yă yi ƙarfi fiye da masu mulki goma a cikin birni.
20 Car il n’y a pas sur terre d’homme juste qui fasse le bien sans jamais pécher.
Babu mai adalci a duniya wanda yake yin abin da yake daidai da bai taɓa yin zunubi ba.
21 Ne fais pas non plus attention à toutes les paroles qui se disent, de peur que tu n’entendes ton serviteur te maudire;
Kada ka mai da hankali ga dukan abin da mutane suke faɗi, in ba haka ba wata rana za ka ji bayinka suna zaginka.
22 car ton cœur sait que bien des fois aussi tu as maudit les autres.
Gama kai kanka ka sani cewa sau da yawa ka zagi waɗansu.
23 J’ai reconnu vrai tout cela par la sagesse; j’ai dit: je veux être sage! mais la sagesse est restée loin de moi.
Dukan waɗannan na gwada su ta wurin hikima na kuma ce, “Na ƙudurta in zama mai hikima,” amma abin ya fi ƙarfina.
24 Ce qui arrive est lointain, profond, profond: qui peut l’atteindre?
Ko da me hikima take, Abin ya yi mana zurfi ƙwarai, yana da wuyar ganewa, wa zai iya gane shi?
25 Je me suis appliqué et mon cœur a cherché à connaître, à sonder et à poursuivre la sagesse et la raison des choses, et j’ai reconnu que la méchanceté est une démence, et qu’une conduite folle est un délire.
Saboda haka na mai da hankalina ga fahimi, don in bincika in nemi hikima da yadda aka tsara abubuwa, in kuma fahimci wawancin mugunta da haukar wauta.
26 Et j’ai trouvé plus amère que la mort la femme dont le cœur est un piège et un filet, et dont les mains sont des liens; celui qui est agréable à Dieu lui échappe, mais le pécheur sera enlacé par elle.
Sai na iske wani abin da ya fi mutuwa ɗaci mace wadda take tarko ne, wadda zuciyarta tarko ne wadda kuma hannuwanta sarƙa ne. Mutumin da ya gamshi Allah zai tsere mata, amma za tă kama mai zunubi.
27 Vois, j’ai trouvé ceci, dit l’Ecclésiaste, en considérant les choses une à une pour en découvrir la raison,
Malami ya ce, “Duba, abin da na gane ke nan. “Na tara abu guda da wani, don in gane tsarin abubuwa,
28 que mon âme a constamment cherchée, sans que je l’aie trouvée: J’ai trouvé un homme entre mille, mais je n’ai pas trouvé une femme dans le même nombre.
yayinda nake cikin nema amma ban samu ba, sai na sami adali guda cikin dubu, amma ba mace mai adalci guda a cikinsu duka.
29 Seulement, vois, j’ai trouvé ceci: C’est que Dieu a fait l’homme droit, mais eux cherchent beaucoup de subtilités.
Wannan ne kaɗai abin da na gane. Allah ya yi mutum tsab amma sai muka rikitar da kanmu.”

< Ecclésiaste 7 >