< 2 Samuel 17 >

1 Achitophel dit à Absalom: « Laisse-moi choisir douze mille hommes; je me lèverai et je poursuivrai David cette nuit même et,
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 tombant sur lui à l’improviste pendant qu’il est fatigué et que ses mains sont affaiblies, je l’épouvanterai, et tout le peuple qui est avec lui s’enfuira; je frapperai alors le roi seul,
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 et je ramènerai à toi tout le peuple: l’homme à qui tu en veux vaut le retour de tous; et tout le peuple sera en paix. »
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 Ce discours plut à Absalom et à tous les anciens d’Israël.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 Cependant Absalom dit: « Appelez encore Chusaï l’Arachite et que nous entendions ce que lui aussi a dans la bouche. »
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 Chusaï vint auprès d’Absalom, et Absalom lui dit: « Voici comment a parlé Achitophel; devons-nous faire ce qu’il a dit? Sinon, parle à ton tour. »
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 Chusaï répondit à Absalom: « Pour cette fois, le conseil qu’a donné Achitophel n’est pas bon. »
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 Et Chusaï ajouta: « Tu sais que ton père et ses gens sont des braves; ils sont exaspérés comme le serait dans la campagne une ourse privée de ses petits. Ton père est un homme de guerre, et il ne passe pas la nuit avec le peuple.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Voici que maintenant il est caché dans quelque ravin ou dans quelque autre lieu. Et si, dès le commencement, il tombe quelques-uns des vôtres, on l’apprendra et l’on dira: Il y a eu une déroute dans le peuple qui suit Absalom.
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 Alors, même le plus vaillant, son cœur fût-il comme un cœur de lion, sera découragé; car tout Israël sait que ton père est un héros, et que ceux qui l’accompagnent sont des braves.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 Je conseille donc que tout Israël se rassemble auprès de toi, depuis Dan jusqu’à Bersabée, multitude pareille au sable qui est sur le bord de la mer; et tu marcheras en personne au combat.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 Nous l’atteindrons en quelque lieu qu’il se trouve, et nous tomberons sur lui comme la rosée tombe sur le sol, et nous ne laisserons échapper ni lui, ni aucun de tous les hommes qui sont avec lui.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 S’il se retire dans une ville, tout Israël apportera des cordes vers cette ville, et nous la traînerons jusqu’au torrent, jusqu’à ce qu’on n’y trouve plus même une pierre. »
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 Absalom et tous les gens d’Israël dirent: « Le conseil de Chusaï l’Arachite vaut mieux que le conseil d’Achitophel. » Yahweh avait décidé de rendre vain le bon conseil d’Achitophel, afin que Yahweh amenât le malheur sur Absalom.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 Chusaï dit aux prêtres Sadoc et Abiathar: « Achitophel a donné tel et tel conseil à Absalom et aux anciens d’Israël, et moi j’ai donné tel et tel conseil.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Envoyez donc de suite informer David, et faites-lui dire: Ne passe pas la nuit dans les plaines du désert, mais hâte-toi de traverser, de peur qu’il n’y ait un suprême désastre pour le roi et pour tout le peuple qui est avec lui. »
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 Jonathas et Achimaas se tenaient à En-Rogel; la servante allait les informer, et eux-mêmes allaient donner avis au roi David; car ils ne pouvaient se faire voir en entrant dans la ville.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 Un jeune homme les ayant aperçus, il le rapporta à Absalom. Mais ils se hâtèrent tous deux de partir, et ils arrivèrent à Bahurim, dans la maison d’un homme qui avait une citerne dans sa cour, et ils y descendirent.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 La femme prit une couverture, qu’elle étendit au dessus de la citerne, et elle y répandit du grain pilé, en sorte qu’on ne remarquait rien.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 Les serviteurs d’Absalom entrèrent chez la femme dans la maison, et dirent: « Où sont Achimaas et Jonathas? » La femme leur répondit: « Ils ont passé le ruisseau. » Ils cherchèrent et, ne les trouvant pas, ils retournèrent à Jérusalem.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 Après leur départ, Achimaas et Jonathas remontèrent de la citerne, et allèrent informer le roi David. Ils dirent à David: « Levez-vous et hâtez-vous de passer l’eau, car Achitophel a donné tel conseil contre vous. »
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 David et tout le peuple qui était avec lui, s’étant levés, passèrent le Jourdain; au point du jour, il n’en restait pas un seul qui n’eût passé le Jourdain.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 Quand Achitophel vit que son conseil n’était pas suivi, il sella son âne, et se leva pour s’en aller chez lui dans sa ville; puis, après avoir donné ses ordres à sa maison, il s’étrangla, et mourut; et on l’enterra dans le tombeau de son père.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 David arriva à Mahanaïm; et Absalom passa le Jourdain, lui et tous les hommes d’Israël avec lui.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 Absalom avait mis à la tête de l’armée Amasa, à la place de Joab; Amasa était fils d’un homme appelé Jéthra, l’Ismaélite, qui était allé vers Abigaïl, fille de Naas, sœur de Sarvia, la mère de Joab.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 Ainsi Israël et Absalom campaient dans le pays de Galaad.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 Lorsque David fut arrivé à Mahanaïm, Sobi, fils de Naas, de Rabba des fils d’Ammon, Machir, fils d’Ammiel de Lodabar, et Berzellaï, le Galaadite, de Rogelim,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 vinrent lui offrir des lits, des plats, des vases de terre, du froment, de l’orge, de la farine, du grain rôti, des fèves, des lentilles, du grain rôti,
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 du miel, du beurre, des brebis et des fromages de vache: ils apportèrent ces choses en nourriture à David et au peuple qui était avec lui, car ils disaient: « Ce peuple a souffert de la faim, de la fatigue et de la soif dans le désert. »
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Samuel 17 >