< 2 Rois 5 >

1 Naaman, chef de l’armée du roi de Syrie, était auprès de son maître un homme puissant et considéré, car c’était par lui que Yahweh avait accordé le salut aux Syriens; mais cet homme fort et vaillant était lépreux.
Na’aman babban hafsan hafsoshin rundunar sarkin Aram ne, kuma ƙasaitaccen mutum ne mai martaba a idon maigidansa, domin ta wurinsa Ubangiji ya ba Aram nasara. Na’aman jarumi ne ƙwarai, amma yana da kuturta.
2 Or les Syriens, étant sortis par bandes, avaient emmené captive une petite fille du pays d’Israël, qui était au service de la femme de Naaman.
To, daga cikin hare haren da mutanen Aram suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra’ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na’aman aiki.
3 Elle dit à sa maîtresse: « Oh! Si mon seigneur était auprès du prophète qui est à Samarie, le prophète le délivrerait de sa lèpre. »
Sai ta ce wa uwargijiyarta, “Da dai shugabana zai ga annabin da yake Samariya, da annabin zai warkar da shi daga kuturtarsa.”
4 Naaman vint rapporter ce propos à son maître, en disant: « La jeune fille du pays d’Israël a parlé de telle et telle manière. »
Sai Na’aman ya je wurin maigidansa ya faɗa masa abin da yarinyan nan daga Isra’ila ta faɗa.
5 Et le roi de Syrie dit: « Va, et j’enverrai une lettre au roi d’Israël. » Il partit, prenant avec lui dix talents d’argent, six mille sicles d’or et dix vêtements de rechange.
Sarkin Aram ya ce, “Ko ta ƙaƙa, ka tafi, zan aika da wasiƙa ga sarkin Isra’ila.” Sai Na’aman ya tashi, ɗauke da talenti goma na azurfa, shekel dubu shida na zinariya, da tufafi kashi goma.
6 Il porta au roi d’Israël la lettre où il était dit: « Or donc, quand cette lettre te sera parvenue, voici que tu sauras que je t’envoie Naaman, mon serviteur, pour que tu le délivres de sa lèpre. »
Wasiƙar da ya kai wa sarkin Isra’ila ta ce, “Da wannan wasiƙa ina aika Na’aman gare ka don ka warkar da kuturtarsa.”
7 Après avoir lu la lettre, le roi d’Israël déchira ses vêtements et dit: « Suis-je un dieu, capable de faire mourir et de faire vivre, qu’il envoie vers moi pour que je délivre un homme de sa lèpre? Sachez donc et voyez qu’il me cherche querelle. »
Da sarkin Isra’ila ya karanta wasiƙar, sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne? Zan iya ɗauke rai ko in mai da shi? Me ya sa wannan mutum ya turo mini wannan mutum in warkar da kuturtarsa? Dubi fa yadda yake nemana da faɗa!”
8 Lorsqu’Elisée, homme de Dieu, apprit que le roi d’Israël avait déchiré ses vêtements, il envoya dire au roi: « Pourquoi as-tu déchiré tes vêtements? Qu’il vienne donc à moi, et il saura qu’il y a un prophète en Israël. »
Da Elisha mutumin Allah ya ji cewa sarkin Isra’ila ya yayyage tufafinsa, sai ya aika masa da wannan saƙo, “Don me za ka yayyage tufafinka? Ka sa mutumin yă zo wurina, zai kuwa san cewa akwai annabi a Isra’ila.”
9 Naaman vint avec ses chevaux et son char, et il s’arrêta à la porte de la maison d’Elisée.
Saboda haka Na’aman ya tafi da dawakansa da keken yaƙinsa, ya tsaya a ƙofar gidan Elisha.
10 Elisée lui envoya un messager pour lui dire: « Va, et lave-toi sept fois dans le Jourdain; ta chair te reviendra, et tu seras pur. »
Sai Elisha ya aika’yan saƙo su ce masa, “Je, ka nutse sau bakwai a Urdun, fatar jikinka za tă koma daidai, ka kuma tsarkaka.”
11 Naaman fut irrité, et il s’en alla, en disant: « Voici que je me disais: Il sortira vers moi, il se présentera lui-même, il invoquera le nom de Yahweh, son Dieu, il agitera sa main sur la plaie et délivrera le lépreux.
Amma Na’aman ya tashi daga can da fushi yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ne wurina yă tsaya, yă yi kira bisa ga sunan Ubangiji Allahnsa, yă kaɗa hannunsa inda kuturtar take, yă warkar da ni.
12 Les fleuves de Damas, l’Abana et le Pharphar, ne valent-ils pas mieux que toutes les eaux d’Israël? Ne pourrais-je pas m’y laver et devenir pur? » Et se tournant, il s’en allait en colère.
Ashe, Amana da Farfa, kogunan da suke Damaskus, ba su fi dukan ruwan da suke Isra’ila ba? Me zai sa ba zan nutse cikinsu in tsarkaka ba?” Sai ya juya ya yi tafiyarsa da fushi.
13 Ses serviteurs s’approchèrent pour lui parler, et ils dirent: « Mon père, si le prophète t’avait demandé quelque chose de difficile, ne l’aurais-tu pas fait? Combien plus dois-tu lui obéir, quand il t’a dit: Lave-toi, et tu seras pur? »
Sai bayin Na’aman suka je kusa da shi suka ce, “Baba, da a ce annabin ya ce ka yi wani abu mai wuya, da ba za ka yi ba? Balle fa cewa kawai ya yi, ‘Ka yi wanka ka kuma tsarkaka’!”
14 Il descendit et se plongea sept fois dans le Jourdain, selon la parole de l’homme de Dieu; et sa chair redevint comme la chair d’un petit enfant, et il fut purifié.
Saboda haka Na’aman ya je ya nutse sau bakwai a Urdun, yadda mutumin Allah ya ce masa, sai fatarsa ta koma kamar ta ɗan yaro.
15 Naaman retourna vers l’homme de Dieu, avec toute sa suite. Quand il fut arrivé, il se présenta devant lui et dit: « Voici donc que je sais qu’il n’y a pas de Dieu sur toute la terre, si ce n’est en Israël. Et maintenant, accepte donc un présent de la part de ton serviteur. »
Sai Na’aman da dukan masu hidimarsa suka koma wurin mutumin Allah. Na’aman ya tsaya a gaban mutumin Allah ya ce, “Yanzu na san cewa babu wani Allah a duk duniya sai a Isra’ila. Ina roƙonka ka karɓi kyauta daga hannun bawanka.”
16 Elisée répondit: « Aussi vrai que Yahweh devant qui je me tiens est vivant, je n’accepterai pas! » Naaman le pressant d’accepter, il refusa.
Annabin ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji wanda nake bauta masa yana a raye, ba zan karɓi kome ba.” Ko da yake Na’aman ya yi ta roƙonsa, amma ya ƙi.
17 Et Naaman dit: « Sinon, permets que l’on donne de la terre à ton serviteur, la charge de deux mulets; car ton serviteur ne veut plus offrir à d’autres dieux ni holocauste ni sacrifice, si ce n’est à Yahweh.
Sai Na’aman ya ce, “In ba za ka karɓa ba, ina roƙonka, bari a ba wa bawanka ƙasa gwargwadon abin da jakuna biyu za su iya ɗauka, gama bawanka ba zai sāke yin hadaya ta ƙonawa, ko wata hadaya ga wani allah ba, sai ga Ubangiji.
18 Toutefois, que Yahweh pardonne ceci à ton serviteur: Quand mon maître entre dans la maison de Remmon pour y adorer, et qu’il s’appuie sur ma main, je me prosterne aussi dans la maison de Remmon; daigne Yahweh pardonner à ton serviteur si je me prosterne dans la maison de Remmon! »
Amma ina fata Ubangiji zai gafarta wa bawanka saboda abu guda. Bari yă gafarta mini sa’ad da na raka sarkina zuwa haikalin Rimmon domin yă yi sujada, bari Ubangiji yă yi wa bawanka gafara saboda wannan.”
19 Elisée lui dit: « Va en paix. » Et Naaman quitta Elisée. Il était à une certaine distance,
Sai Elisha ya ce, “Ka sauka lafiya.” Bayan Na’aman ya yi ɗan nisa,
20 lorsque Giézi, serviteur d’Elisée, homme de Dieu, dit en lui-même: « Voici que mon maître a ménagé Naaman, ce Syrien, en n’acceptant pas de sa main ce qu’il avait apporté. Yahweh est vivant! Je vais courir après lui et j’en obtiendrai quelque chose. »
sai Gehazi, bawan Elisha mutumin Allah, ya yi tunani a ransa ya ce, “Maigidana ya yi wa Na’aman mutumin Aram nan ƙaramci da bai karɓi duk abin da ya kawo ba. Muddin Ubangiji yana a raye, zan bi shi a guje in karɓi wani abu daga gare shi.”
21 Et Giézi se mit à poursuivre Naaman. Naaman, le voyant courir après lui, descendit de son char pour aller à sa rencontre, et il dit: « Tout va-t-il bien? »
Saboda haka Gehazi ya bi Na’aman a guje. Da Na’aman ya hango shi yana zuwa a guje, sai ya sauka daga keken yaƙinsa ya tarye shi ya ce, “Lafiya?”
22 Giézi répondit: « Tout va bien! Mon maître m’envoie te dire: Voici que viennent d’arriver chez moi deux jeunes gens de la montagne d’Ephraïm, d’entre les fils des prophètes; donne pour eux, je te prie, un talent d’argent et deux vêtements de rechange. »
Gehazi ya amsa ya ce, “Lafiya ƙalau. Maigidana ne ya aiko ni cewa, ‘Samari biyu daga ƙungiyar annabawa sun ziyarce ni daga ƙasa mai duwatsu na yankin Efraim. Ina roƙonka ka ba su talenti na azurfa da tufafi kashi biyu.’”
23 Naaman dit: « Consens à prendre deux talents. » Il le pressa d’accepter et, ayant serré deux talents d’argent dans deux sacs avec deux habits de rechange, il les remit à deux de ses serviteurs pour les porter devant Giézi.
Na’aman ya ce, “Ba damuwa, karɓi talenti biyu.” Ya roƙi Gehazi yă karɓa, sa’an nan ya ƙunsa masa talentin biyu na azurfa ya sa masa a kan jakankuna biyu, ya haɗa da tufafi kashi biyu, ya ba bayinsa biyu suka ɗauka, ya ce su sha gaban Gehazi.
24 Arrivé à la colline, Giézi les prit de leurs mains et les déposa dans la maison, puis il renvoya les hommes, qui partirent.
Da Gehazi ya isa wani tudu, sai ya karɓi kayan daga wurin bayin ya shiga da su a ɓoye a cikin gida. Sa’an nan ya sallami mutanen suka tafi.
25 Et il alla se présenter à son maître. Elisée lui dit: « D’où viens-tu, Giézi? » Il répondit: « Ton serviteur n’est allé ni d’un côté ni d’un autre. »
Sa’an nan ya shiga ya tsaya a gaban maigidansa Elisha. Sai Elisha ya tambaye shi ya ce, “Ina ka je, Gehazi?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Bawanka bai je ko’ina ba.”
26 Mais Elisée lui dit: « Mon esprit n’est-il pas allé avec toi, lorsque cet homme a quitté son char pour venir à ta rencontre? Est-ce le moment d’accepter de l’argent, et d’accepter des vêtements et des oliviers et des vignes et des brebis et des bœufs et des serviteurs et des servantes?
Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba sa’ad da mutumin ya sauko daga keken yaƙinsa ya tarye ka. Kana gani wannan lokaci ne da za a karɓi kuɗi, da riguna, da gonar inabi, da tumaki, da bijimai, da bayi maza da mata?
27 La lèpre de Naaman s’attachera à toi et à ta postérité pour toujours. » Et Giézi sortit de la présence d’Elisée avec une lèpre blanche comme la neige.
Kuturtar Na’aman zai manne maka da zuriyarka har abada.” Sai Gehazi ya fita daga gaban Elisha a kuturce, fari fat kamar dusar ƙanƙara.

< 2 Rois 5 >